Wanda ya jagoranci sallar juma’a a yau a birnin Tehran  Hujjatul-Islam Wal Muslimin Muhammmad Hassan Abu Turabi Fard, ya ce; makiyan jamhuriyar musulunci ta Iran suna magana da sauti daya,yayin da juyin juya halin musulunci na Iran ya hada kasashen Lebanon,Yemen, Falasdinu,Iraki da wasu kasashen musulmi.

Limamin na Tehran ya kara da cewa, lokaci ya yi da al’ummar musulmi za su yi watsi da duk wani sabani a tsakaninsu, su dunkule su rika Magana da yawu daya.

Dangane da karatowar watan Ramadan mai alfarma, limamin na Tehran ya ce, watan Ramadan mai alfarma, wata ne na kara kulla alaka da Allah madaukakin sarki da karatun al’kur’ani.

Hujjatul Islam Wal Muslimin Abu Turabi ya kuma ce; Ma’abota alkur’ani mai girma su ne wadanda aka sani da yin rayuwa ta hankali da ilimi, kuma sakamakon wannan irin raywua shi ne samar da hadin kai da nesantar rabuwar kawuna.

Bugu da kari, limanin na Tehran ya ce hadin kai yana daga cikin sakamakon kare hakkin bil’adama, domin alkur’ani mai girma ya kiraye mu baki daya da mu kasance a tare da gaskiya da kuma tsarin musulunci.

Dangane da abinda Amurk ta mayar da hankali akansa a kiyayyarta da Iran, limamin ya ce  shi ne yakin kwakwalwa da kuma farfaganda.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: na Tehran ya

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Ci gaba da killace Gaza da kuma kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, laifi ne da ba a taba yin irinsa ba a tarihin dan Adam

A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Masar Badar Abdel Ati a yammacin jiya Lahadin da ta gabata, Araqchi ya bayyana ci gaba da killace yankin Gaza da rashin abinci da magunguna, tare da kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, a matsayin wani laifi da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin dan Adam. Ya dauki Amurka da sauran masu goyon bayan ‘yan sahayoniyya a matsayin masu hannu a kisan kiyashi da laifukan yaki da ake aikatawa a Gaza.

Ministan harkokin wajen na Iran ya jaddada wajibcin tunkarar muggan manufofin yahudawan sahayoniyya na tilastawa al’ummar Gaza da yammacin kogin Jordan yin hijira daga muhallinsu, yana mai bayyana halin ko in kula da kasashen duniya suke nun awa kan wadannan laifuka a matsayin abin mamaki da damuwa.

Araghchi ya kuma yi wa takwaransa na Masar bayani kan ci gaban tattaunawar Iran da Amurka kan Shirin makamashin nukiliya na zaman lafiya da ake takaddama a kai tsawon shekaru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya