Kungiyar M23 Ta Kwace Wani Birni Na Biyu A Gabashin DR Congo
Rahotanni daga Congo na cewa Kungiyar yan tawayen DR Congo ta M23 ta kutsa birnin Bukavu birnin mafi girma a gabashin kasar, inda ta kwace ofishin gwamnan lardin.
Bayanai sun ce mayakan sun kutsa cikin birnin ba tare da fuskantar wata tirjiya ba, kuma sun samu tarba mai kayu daga jama’ar yankin.
Bukavu shi ne birni na biyu mafi girma a yankin da ƴan tawayen suka karbe bayan Goma mai kunshe da albarkatun kasa.
A ranar Juma’a ne mayakan suka kame filin jirgin saman birnin na Bukavu da ke da tazarar kilomita 30 arewa da birnin – daga nan kuma sai suka nufi birnin wanda shi ne babban birnin lardin Kudancin Kivu.
Gwamnatin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo (DRC), ta yi Allah wadai da shigar kungiyar ‘yan tawaye ta M23 cikin Bukavu, inda ‘yan tawayen sun kwace iko da muhimman wurare da dama.
Cikin wata sanarwa, gwamnatin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ta tabbatarwa al’umma cewa tana bibiyar yanayin da ake ciki a Bukavu, hedkwatar lardin Kivu ta kudu, inda ‘yan tawayen suka shiga.
Gwamnatin dai ta nanata kudurinta na tabbatar da oda da tsaro da cikakken ikonta, tana mai kira ga mazauna Bukavu su zauna a gida.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Sanarwar ta ce, “A ranar 2 ga Oktoba, 2025, misalin karfe 08:25 na safe, wani mutumin kirki ya kai rahoton kisan gilla a ofishin D Dibisional Police Headkuarters.
“Rahoton ya bayyana cewa wasu mutane biyu sun je gidan wani Ahmad Lawan, namiji, mai shekaru 29, wanda ake kira Soje, mazaunin Sabon Kasuwa, wanda ake zarginsa a matsayin shahararren dan sara-suka.”
“Suka kwankwasa kofar gidansa, bayan da ya bude, sai suka soka masa wuka a kirji sannan suka tsere zuwa wani wuri da ba a sani ba.”
Wakili ya bayyana cewa jami’an da ke karkashin D’ Dibision, karkashin jagorancin DPO CSP Mubarak Sani Baba, “sun hanzarta zuwa wurin da abin ya faru, suka dauki wanda abin ya shafa zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH), Bauchi, inda likita ya tabbatar da rasuwarsa.”
Ya kara da cewa an mika gawar ga iyalansa domin a yi masa jana’iza bisa tsarin Musulunci.
A cewar binciken farko, ‘yansanda sun gano Abubakar Ibrahim, wanda aka fi sani da Duduwa, da Abubakar Mohammed, a matsayin manyan masu hannu a kisan.
Bayan an binne Lawan, Wakil ya ce wasu fusatattun matasa sun kai farmakin ramuwar gayya inda suka kona gidan iyalin daya daga cikin wadanda ake zargi.
“Amma hadakar jami’an Rapid Response Skuad, Operation Restore Peace da D’ Dibision suka iso da gaggawa suka dakile rikicin,” in ji shi.
‘Yansanda sun kara bayyana cewa daya daga cikin manyan wadanda ake zargi, Abubakar Ibrahim (Duduwa), wanda ya fara tserewa, daga baya an gan shi yana yawo a Mararraban Liman-Katagum, kuma jami’an tsaro na sa-kai suka kama shi.
“Yayin da ake kai shi ofishin ‘yansanda, wasu fusatattun matasa suka tare su a Kwanar Kwaila suka kai masa hari da takubba, wanda ya jawo karaya a hannuwansa biyu da kuma mummunan rauni a kansa,” in ji Wakil.
Ya ce jami’an ‘yansanda sun iso da gaggawa inda suka ceci wanda ake zargin, suka tarwatsa matasan, sannan suka garzaya da shi ATBUTH domin jinya.
Sanarwar ta kara da cewa duk wadanda aka kama suna kan bincike domin tantance irin rawar da kowane dayansu ya taka a lamarin.
Wakil ya ruwaito Kwamishinan ‘Yansanda, CP Sani-Omolori Aliyu, yana gargadin iyaye da shugabannin al’umma da su ja kunnen ‘ya’yansu kada su bari a yi amfani da su wajen tayar da hankalin jama’a.
“Rundunar ba za ta yi wata-wata ba wajen daukar mataki mai tsauri kan duk wanda ko wata kungiya da gangan ta kawo tabarbarewar doka da oda ta kowace siga. Duk wanda aka kama da laifi za a hukunta shi bisa cikakkiyar doka,” in ji Aliyu.
Ya kara da cewa an tura tawagogin jami’an musamman a sassa daban-daban na jihar domin tabbatar da bin doka da oda yadda ya kamata.
A tuna cewa, kamar yadda jaridar PUNCH Metro ta ruwaito a 2024, rundunar ta taba kama wasu mutane makamantan wadannan bayan kisan gilla da aka yi wa wani Adamu Alkasim a unguwar Bayan Gari, Bauchi.
A lokacin, an kama mutum biyu Usman Shehu, mai shekara 20, da Abdullahi Abubakar, mai shekara 19, bisa zargin “hada baki wajen aikata laifi da kuma kisan kai.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA