HausaTv:
2025-06-04@01:32:07 GMT

Masu Alaka

Published: 17th, February 2025 GMT

Kungiyar M23 Ta Kwace Wani Birni Na Biyu A Gabashin DR Congo

Rahotanni daga Congo na cewa Kungiyar yan tawayen DR Congo ta M23 ta kutsa birnin Bukavu birnin mafi girma a gabashin kasar, inda ta kwace ofishin gwamnan lardin.

Bayanai sun ce mayakan sun kutsa cikin birnin ba tare da fuskantar wata tirjiya ba, kuma sun samu tarba mai kayu daga jama’ar yankin.

Bukavu shi ne birni na biyu mafi girma a yankin da ƴan tawayen suka karbe bayan Goma mai kunshe da albarkatun kasa.

A ranar Juma’a ne mayakan suka kame filin jirgin saman birnin na Bukavu da ke da tazarar kilomita 30 arewa da birnin – daga nan kuma sai suka nufi birnin wanda shi ne babban birnin lardin Kudancin Kivu.

Gwamnatin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo (DRC), ta yi Allah wadai da shigar kungiyar ‘yan tawaye ta M23 cikin Bukavu, inda ‘yan tawayen sun kwace iko da muhimman wurare da dama.

Cikin wata sanarwa, gwamnatin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo ta tabbatarwa al’umma cewa tana bibiyar yanayin da ake ciki a Bukavu, hedkwatar lardin Kivu ta kudu, inda ‘yan tawayen suka shiga.

Gwamnatin dai ta nanata kudurinta na tabbatar da oda da tsaro da cikakken ikonta, tana mai kira ga mazauna Bukavu su zauna a gida.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya gana da shugaban kasar Masar a birnin Alkahira

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya gana da shugaban kasar Masar Abdel Fattah el-Sisi a yau Litinin.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arakchi ya isa birnin Alkahira da yammacin jiya Lahadi domin tattaunawa da manyan jami’an kasar Masar.

A yayin wannan ziyara, Araqchi ya gana da ministan harkokin wajen Masar Badr Abdel Aty da shugaban kasar Masar Abdel Fattah el-Sisi inda suka tattauna batutuwan baya-bayan nan a dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da ci gaban yankin, musamman batun kalubalantar laifukan haramtacciyar kasar Isra’ila, da kuma wasu batutuwan kasa da kasa.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya sanar da Shirin ministan harkokin wajen Iran na ziyartar ministan harkokin wajen kasar Masar da Lebanon a wani taron manema labarai da ya kira a yammacin ranar Asabar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aragchi: Iran Tana Goyon Bayan Tattaunawa Saboda Hadin Kai Tsakanin Mutanen Lebanon
  • Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Soki Rahoton Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Kan Kasarsa
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Wani Kisan Kiyashi Kan Masu Bukatar Kayan Agaji
  • Masu Sayar da Rago Sun Koka A Zamfara Saboda Karancin Masaya
  • Ana samun Karancin Masu Sayen Dabbobi A Kano Duk Karatowar Sallar Layya
  • Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yana Ziyarar Aiki A Kasar Masar, inda Ya Gana Da Shugaban Kasar
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Taron Kungiyar BRICS Zai Kawo Bunkasar Tattalin Arziki
  • Ma’aikatar Lafiyar Sudan Ta Ce: An Dan Samu Ja Da Baya A Cutar Kwalara Da Ta Kunno Kai A Kasar