Aminiya:
2025-04-30@23:28:57 GMT

Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe

Published: 17th, February 2025 GMT

’Yan sanda sun yi nasarar kama wasu mutane biyu da ake zargi da laifin yi wa wata yarinya ‘yar shekara 12 fyaɗe a kauyen Jalingo da ke Ƙaramar Hukumar Tarmuwa a Jihar Yobe.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, ya fitar a Damaturu ranar Litinin.

Gwamnati ta raba wa mata tallafin awakai na N5bn a Katsina Yadda na yi wa budurwar da muka haɗu a Facebook gunduwa-gunduwa —Matashi

Ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:30 na yammacin ranar 15 ga watan Fabrairu, inda waɗanda ake zargin suka kai yarinyar wani kango a jeji suka keta mata haddi.

Rahoton na cewar, “Hedikwatar ‘yan sandan jihar reshen Ƙaramar Hukumar Tarmuwa ta cafke waɗanda ake zargin da suka haɗa baki tare da yi wa yarinyar ‘yar shekara 12 fyade, inda suka ji mata munanan raunuka.”

“Kamar yadda majiyar ke nunawa tuni wannan yarinya ta samu kulawa cikin gaggawa, yayin da aka miƙa waɗanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na jiha (SCID) da ke Damaturu domin gudanar da bincike mai zurfi akan su,” in ji Abdulkarim.

Haka nan a wani samame da aka yi, kakakin ya ce an kuma kama wasu ɓata gari uku a unguwar Alimari da ke Damaturu bisa zargin ɗauke wani babur tare da lalata shi kwanan nan a unguwar Abbari da ke cikin birnin na Damaturu.

A cewarsa, waɗanda ake zargin sun ɓoye babur ɗin ne da wasu kayayyaki a wani gini da ba a kammala ba a yankin.

Ya ce jami’an nasu da ke aiki a ofishin ‘yan sanda na A Divisional, sun kai farmaki gidan tare da cafke waɗanda ake zargi da aikata laifin satar babur ɗin.

Har ila yau, SP Abdulkarim ya ce hedikwatar ‘yan sanda ta Gujba tare da haɗin gwiwar ‘yan banga sun ceto wani matashi daga hannun masu garkuwa da mutane a ƙauyen Daddawel.

Ya ce matashin da aka yi garkuwa da shi a ranar 12 ga watan Fabrairu, ya shakami iskar ’yanci ne bayan wani artabu tsakanin masu garkuwar da ‘yan sanda da ‘yan sa kai, lamarin da ya tilasta wa masu laifin gudu suka bar wanda aka yi garkuwar da sauran kayayyaki ciki har da wata bindiga guda ɗaya.

Abdulkarim ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya yaba da ƙoƙarin jami’an rundunar, inda ya ba da tabbacin ɗorewar yaƙi da miyagun laifuka a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: fyaɗe Jihar Yobe yarinya waɗanda ake zargin

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno

Wata majiya kuma ta bayyana cewa adadin mutanen da suka mutu na iya fin haka, duba da yawan mata da yara da lamarin ya rutsa da su.

A lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomin soji da ‘yansanda ba su fitar da wata sanarwa ba dangane da lamarin ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Najeriya Wajen Yin Watsi Da Kariyar Cinikayya Da Yin Adawa Da Danniya Da Cin Zarafi
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
  • Sojoji Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace, Sun Ƙwato Shanu 32 A Katsina
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Mutum 8 Da Bam A Borno
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya