Mutum biyu sun shiga hannu kan yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Yobe
Published: 17th, February 2025 GMT
’Yan sanda sun yi nasarar kama wasu mutane biyu da ake zargi da laifin yi wa wata yarinya ‘yar shekara 12 fyaɗe a kauyen Jalingo da ke Ƙaramar Hukumar Tarmuwa a Jihar Yobe.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, ya fitar a Damaturu ranar Litinin.
Ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:30 na yammacin ranar 15 ga watan Fabrairu, inda waɗanda ake zargin suka kai yarinyar wani kango a jeji suka keta mata haddi.
Rahoton na cewar, “Hedikwatar ‘yan sandan jihar reshen Ƙaramar Hukumar Tarmuwa ta cafke waɗanda ake zargin da suka haɗa baki tare da yi wa yarinyar ‘yar shekara 12 fyade, inda suka ji mata munanan raunuka.”
“Kamar yadda majiyar ke nunawa tuni wannan yarinya ta samu kulawa cikin gaggawa, yayin da aka miƙa waɗanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na jiha (SCID) da ke Damaturu domin gudanar da bincike mai zurfi akan su,” in ji Abdulkarim.
Haka nan a wani samame da aka yi, kakakin ya ce an kuma kama wasu ɓata gari uku a unguwar Alimari da ke Damaturu bisa zargin ɗauke wani babur tare da lalata shi kwanan nan a unguwar Abbari da ke cikin birnin na Damaturu.
A cewarsa, waɗanda ake zargin sun ɓoye babur ɗin ne da wasu kayayyaki a wani gini da ba a kammala ba a yankin.
Ya ce jami’an nasu da ke aiki a ofishin ‘yan sanda na A Divisional, sun kai farmaki gidan tare da cafke waɗanda ake zargi da aikata laifin satar babur ɗin.
Har ila yau, SP Abdulkarim ya ce hedikwatar ‘yan sanda ta Gujba tare da haɗin gwiwar ‘yan banga sun ceto wani matashi daga hannun masu garkuwa da mutane a ƙauyen Daddawel.
Ya ce matashin da aka yi garkuwa da shi a ranar 12 ga watan Fabrairu, ya shakami iskar ’yanci ne bayan wani artabu tsakanin masu garkuwar da ‘yan sanda da ‘yan sa kai, lamarin da ya tilasta wa masu laifin gudu suka bar wanda aka yi garkuwar da sauran kayayyaki ciki har da wata bindiga guda ɗaya.
Abdulkarim ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar, Garba Ahmed, ya yaba da ƙoƙarin jami’an rundunar, inda ya ba da tabbacin ɗorewar yaƙi da miyagun laifuka a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: fyaɗe Jihar Yobe yarinya waɗanda ake zargin
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
Ya umurci jami’an tsaro su gaggauta kai dauki ba tare da bata lokaci ba don tabbatar da an gurfanar da masu laifin a gaban kuliya, yana mai jaddada cewa za a hukunta duk wanda aka samu dauke da muggan makamai ko kuma aka samu yana da hannu wajen aikata laifuka.
“Ga iyalai da ‘yan uwa da masoyan marigayi Ahmed, ina mika sakon ta’aziyyata, da na gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, kuma muna jimami tare da ku, ina ba ku tabbacin za a yi adalci.
“Ina kuma kira ga jami’an tsaro su kara kaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma sintiri kan tituna, musamman a wuraren da ke fuskantar irin wadannan laifuka. Jama’armu sun cancanci tafiya cikin walwala ba tare da tsoro ko barazana ga rayuka da dukiyoyinsu ba.
“Muna ci gaba da jajircewa wajen kare kowane rai da kuma tabbatar da cewa zaman lafiya da tsaro sun ci gaba da wanzuwa a wannar jiharmu.”
Ya yi kira ga al’umma su tallafa wa jami’an tsaro ta hanyar ba su bayanai masu muhimmanci kan lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp