Ma’aikatar ilimi ta jihar Kano ta fara rangadin tantancewa a kauyukan jihar, gabanin shirin wayar da kan al’umma game da yaran da ba su zuwa makaranta.

Ziyarar na da nufin gano musabbabin wannan matsala tare da nemo mafita ta hanyar hada kai tsakanin al’umma.

Kididdigar da Asusun yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya fitar na nuna da cewa, Kano tana da kimanin yara 837,479 da ba sa zuwa makaranta, adadi mai ban mamaki da jihar ke kokarin magancewa.

 

Tawagar tantancewar, karkashin jagorancin jami’a mai kula da ilimin yara mata ta jihar, Hajiya Amina Kassim, ta ziyarci kauyuka da dama, inda ta tattauna da iyaye, da shugabannin gargajiya, da malaman addini.

“Tawagar ta gano muhimman abubuwan da ke haddasa  yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yankunan karkara, ciki har da talauci, da rashin tsaro, da kuma al’adun zamantakewa”

Mataimakin shugaban kwamitin gudanarwa na makarantun jihar  SBMC, Alhaji Garba Adamu Wudil, ya ce ta hanyar hada kai da al’ummomin yankin da masu ruwa da tsaki, gwamnati na da burin kara fahimtar matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta da kuma kokarin samar da ingantaccen ilimi ga kowa da kowa.

Hakimin kauyen Kafin Malamai a karamar hukumar Garko Mukhtar Aliyu da wakilin hakimin kauyen Bange na Wudil Ya’u Ibrahim Bange sun yabawa kokarin gwamnati mai ci na gyara fannin ilimi.

Sun yi kira ga gwamnati da ta kara samar da karin makarantun sakandire a cikin al’umma domin daukar adadin daliban da suka kammala karamar sakandare (JSS) duk shekara.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, rangadin tantancewar wani muhimmin mataki ne na samar da ingantattun dabaru don rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a jihar Kano.

Daga Khadija Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: yaran da ba sa zuwa makaranta

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici

Gwamnatin Jihar Neja, ta rufe Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBBU) da ke Lapai saboda matsalolin tsaro da suka janyo mutuwar wasu ɗalibai.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Abubakar Usman, ya ce an ɗauki wannan matakin ne saboda rashin tabbacin tsaro da ke barazana ga rayuwar ɗalibai da ma’aikata.

Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum 1447: Yau ce ranar sabuwar shekarar Musulunci – Sarkin Musulmi

Gwamna Umaru Bago ya amince da rufe jami’ar nan take, kuma za ta ci gaba da kasancewa a rufe har sai an samu sauyi.

“Lafiyar kowa, musamman ɗalibai da malamai, na da matuƙar muhimmanci ga gwamnatin Jihar Neja,” in ji sanarwar.

“Mun yi matuƙar baƙin ciki da abin da ya faru, kuma muna ɗaukar matakan gaggawa don magance lamarin.”

Gwamnatin ta roƙi ɗalibai, malamai da ma’aikatan jami’ar su kwantar da hankalinsu, kuma su kasance masu lura, su kuma yi aiki tare da jami’an tsaro a wannan lokaci.

Haka kuma gwamnatin ta tabbatar da cewa tana ɗaukar matakai domin wanzar da zaman lafiya.

Ta ce duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

“Za mu ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’a, da kuma tabbatar da doka da oda a faɗin Jihar Neja,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
  • Ƙarancin Abinci: UNICEF ta tallafa wa yara 600,000 a Borno da Yobe
  • Ƙarancin abinci: UNICEF ta tallafawa yara 600,000 a Borno, Yobe
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya
  • ’Yan sanda sun kama mutum 5 kan kisan Kanawa 2 a Benuwe
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma
  • Arsenal za ta ɗauki ɗan ƙwallon Brentford Christian Norgaard
  • An ɗaure mutum 6 shekaru 120 kan satar yara a Kano