Kungiyar Hamas Ta Jaddada Rashin Yiwuwar Korar Falasdinawa Daga Yankin Zirin Gaza
Published: 12th, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas ta sha alwashin dakile shirin shugaban Amurka Trump na neman tilastawa Falasdina gudun hijira daga Zirin Gaza
Kungiyar Hamas ta lashi takobin dakile shirin shugaban Amurka Donald Trump na neman tilastawa Falasdinawa gudun hijira zuwa kasashe makwabta, tare da yin watsi da barazanar da ya yi na bude kofofin jahannama a yankin Falasdinu idan har Hamas ba ta sako fursunonin yahudawan sahayoniyyar Isra’ila kafin yammacin ranar Asabar ba.
A cikin wata sanarwa da kungiyar Hamas ta fitar ta ce, abin da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kasa cimmawa ta hanyar wuce gona da iri, ba zai yi nasara ba ta hanyar aiwatar da siyasar makirci da yaudara.
Sanarwar ta ce, manyan al’ummar Gaza sun tsaya tsayin daka wajen fuskantar hare-haren bama-bamai da wuce gona da iri, kuma za su ci gaba da tsayin daka kan kasarsu tare da dakile duk wani shiri na neman tilasta musu gudun hijira daga muhallinsu zuwa wasu kasashen makwabta.
Hamas ta jaddada cewa: shirin korar al’ummar Palasdinu daga Gaza ba zai yi nasara ba, kuma zai fuskanci kalubalen Falasdinawa, Larabawa da kuma al’ummar musulmi wadanda suka yi watsi da duk wani shiri na raba Falasdinawa da muhallinsu zuwa gudun hijira.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: gudun hijira
এছাড়াও পড়ুন:
Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
Lamarin ya ci gaba da raguwa har zuwa 2024, inda yawan kudaden da ake kashewa a yawon ketare ya fadi da kaso 14 a matakin shekara-shekara zuwa dala biliyan 2.66.
Hakan na nuni da cewa ‘yan Nijeriya sun rage kashe kudaden da suke kashewa kan safarar jiragen sama da dala biliyan 1.12 ko kuma kashi 30 cikin dari a cikin shekaru biyun.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp