Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Kashe Naira Tiriliyan 4.2 Don Aikin Manyan Hanyoyi
Published: 7th, February 2025 GMT
Wannan ya hada da kilomita 65 daga Legas zuwa Ogun da wani karin da zai tashi daga Kalabar ta Akwa Ibom, wanda titin zai ginu a karkashin ‘Engineering, Procurement, and Construction’ (EPC) da tsarin za su kula da shi na tsawon shekaru goma bayan ginawa.
Majalisar zartarwar ta amince da kashe naira biliyan 470.
Shi kuma babban hanyar Lagos zuwa Ibadan ya samu amincewar naira biliyan 195 domin a gina shi a karkashin asusun shirin inganta hanyoyi na shugaban kasa (PIDF), da ke da manufar rage cunkoso da inganta sufuri a manyan hanyoyin da ake yawan bi.
Sai dai hanyar Abuja zuwa Kano wanda aka jima da bayar da shi ga kamfanin ‘Julius Berger’, yanzu an sake fasalta shi yadda za a samu nasarar kammala aikin a kan lokaci. Ministan ya ce yanzu aikin ya koma kilomita 118 kuma za a sanya wutar layi.
Ministan ya ce dukkanin ayyukan masu inganci ne za a yi kuma da nufin kyautata rayuwar al’ummar kasa da kare rayukan a yayin tafiye-tafiye, ya ba da tabbacin gwamnati na sanya ido wajen gudanar da nagartaccen aiki.
কীওয়ার্ড: Gwamnatin Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
Irabor ya ce, littafin nasa na ƙoƙarin kawo tarihin “tasirin Boko Haram a Nijeriya ta fannoni daban-daban” da kuma “hakikanin gaskiya a kan Boko Haram, wanda na samo a lokacin ina matsayin kwamandan soji na yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya.”
Tsohon babban hafsan tsaron ya ce, babban abinda ya fi tayar da hankali a yaki da Boko Haram shi ne yawan rayukan da aka rasa. A cewarsa, “irin rayukan mutanen da aka kashe a rikicin Boko Haram yana da yawa kuma ana iya kwatanta shi da annoba.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA