Masarautar Fika ta buɗe gasar ƙwallon ƙafa karo na uku a Potiskum
Published: 3rd, February 2025 GMT
Masarautar Fika da ke Jihar Yobe ta buɗe gasar ƙwallon ƙafa karo na uku a filin wasa na Dabo Aliyu da ke garin Potiskum.
An buɗe gasar ƙarƙashin jagorancin mai Martaba Sarkin Fika, Alhaji Dr. Muhammad Ibn Abali Muhammad Idris wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Yobe.
Ya je Maiduguri daga Legas a kan keke Rikicin rusau ya yi ajalin mutum 4 a KanoGasar wacce aka fara a shekarar 2011 ta bunƙasa zuwa wani gagarumin taron wasanni a yankin, wadda ke haɗa ƙungiyoyi daga ƙananan hukumomi huɗu na yankin da suka haɗa da Fune, Potiskum, Fika, da Nangere.
A shekarar 2017 aka gudanar da gasar karo na biyu, lamarin da ya ƙara tabbatar da gasar a matsayin ɗaya daga cikin manyan wasannin ƙwallon kafa a jihar.
A wannan shekarar ta 2025 an buɗe gasar ce da wasa tsakanin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Total Pillars FC Potiskum da Parma FC ita ma a garin na Potiskum.
Ƙungiyoyin biyu dai sun ƙare zagayen farko ba tare da an zura ƙwallo a raga ba, amma ana minti 19 bayan dawowa daga hutun rabin lokaci Abdulzabi na Parma ya zura ƙwallo daya tilo da aka tashi a wasan, inda ƙungiyar tasa ta samu nasara da ci 1-0.
Gasar ta bana ta samu halartar ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa 64 daga ƙananan hukumomi huɗu da suka shiga gasar.
Wani muhimmin abin da ya fi ɗaukar hankali a bikin buɗe gasar shi ne bayar da lambobin yabo ga fitattun mutane domin nuna irin gudunmawar da suke bayarwa wajen wasanni da ci gaban al’ummar wannan masarauta ta Fika.
Waɗanda aka karrama sun haɗa da Alhaji Garba Mohammed, FIFA Lamido, Aliyu Abba Bulama (AFCON), Sadik Rabiu Alkali da Alhaji Ba’aba Abba (Aljino na Fika).
Ana sa ran za a ci gaba da gudanar da gasar nan da makonni masu zuwa, inda za a haɗa haziƙan ’yan ƙwallon ƙafa da masu sha’awar ƙwallon ƙafa daga sassan yankin na Masarautar ta Fika.
Mai Martaba Sarkin Fika, Alhaji Muhammad Ibn Abali Muhammad Idris ya yi fatan alheri ga waɗanda suka samu damar shiga wannan gasa tare da yi musu addu’ar kammala gasar lafiya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Yobe Masarautar Fika ƙwallon ƙafa buɗe gasar
এছাড়াও পড়ুন:
Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
Rahotannin da suke fitowa daga kasar Yemen na cewa katafaren jirgin ruwa mai daukar jiragen saman yaki malakar klasarAmurka wato USS Harry Truman zai fice daga tekun red sea da nan kusa saboda makaman kasar Yemen da suka fada mata.
Tashar talabijin ta Almasirah ta kasar Yemen ta nakalto wani jami’in ma’aikatar tsaron kasar wanda baya son a bayyana sunansa yana cewa, saboda yawan hare haren da sojojin Yemen suka kaiwa jirgin, wadanda suka hada da amfani da makamai masu linzami samfurin Crusse da kuma Balistic, har ila yau da jiragen yaki masu kunan bakin waken da suka fada a kansa. A yanzun ya zama dole jirgin ya fice daga tekun.
Tun cikin watan Maris da ya gabata ne gwamnatin shugaba Trump ta fara kaiwa kasar yemen hare-hare da jiragen sama wadanda suke tashi daga sansanin jiragen yaki da ke kan wannan jirgin. Saboda tilastawa kasar Yemen dakatar da kai hare-hare a kan HKI, don ta kawo karshen tallafawa Falasdinawa a Gaza.
Amma ya zuwa yanzu hare-haren na Amurka sun kasa kaiwa ga bukata, majiyar gwamnatin kasar ta yemen ta ce hare-haren Amurka a kasar ba zasu sa ta dakatar da tallafawa Falasdinawa, da kuma hanata kai hare hare kan jiragen kasuwanci na HKI masu wucewa ta tekun red sea ba.
A wani labarin kuma hare haren na sojojin yemen sun sa wani jiegin yakin Amurka samfurin F-18 ya fada cikin ruwa a tekun na Red Sea a kokarin kaucewa makaman sojojin Yemen.