Aminiya:
2025-08-01@10:29:54 GMT

Ya je Maiduguri daga Legas a kan keke

Published: 3rd, February 2025 GMT

Wani mahayin keken hawa, Samuel Fastuma, ɗan asalin Jihar Benue, ya kammala balaguronsa a kan keken hawa daga Legas zuwa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno a cikin kwanaki 8 kacal.

A cewar Fastuma, ya fara wannan tafiya ce a ranar Lahadi 19 ga watan Janairu, 2025 bisa ƙudirinsa na nuna fatan alheri ga daukacin masu yaƙi da fatara da masu yaƙi da muggan ƙwayoyi da kuma neman hadtin kai da zaman lafiya a tsakanin al’ummar Nijeriya.

Rikicin rusau ya yi ajalin mutum 4 a Kano Alawar yara mai sanya maye ta shiga gari —NDLEA

Da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan isar sa birnin na Maiduguri, Fastuma ya ce, ya fara wannan tafiya ce domin yi wa matasa fatan alheri da kuma yin kira da a zauna lafiya a tsakanin ’yan Nijeriya.

Fastuma ya ce, “ina so in sanar da matasa, cewa abubuwa za su daidaita a cikin kasar nan don haka a cigaba da sa rai a kan hakan.

“Na yi imani cewa, idan kuna da basira, ya kamata ku yi amfani da ita domin hakan kan iya haifar da abubuwa masu girma na ci gaba.

“Tafiyar da na yi ta tsawon kwana takwas, na hadu da kalubale da dama da suka hada da rashin kyawun hanyoyin mota a wasu yankunan.”

Fastuma ya ce, “akwai wasu wurare masu kalubale, musamman tsakanin Bida da Npai, inda titin ba shi da kyau sosai.

“Haka nan na kuma fuskanci wasu matsaloli na bin hanyar Kano zuwa Potiskum.”

Duk da wadannan kalubale Fastuma ya jajirce kuma ya samu nasarar isa Maiduguri a ranar 26 ga watan Janairu.

“Na sha jin labarin Jihar Borno, amma wannan shi ne karo na farko da na kawo ziyara,” in ji shi.

‘‘Tsaro a kan titin ya yi matukar tsauri, kuma ya zuwa yanzu, na gano Jihar Borno wuri ne mai dadin rayuwa.”

Tafiya ta ban mamaki irin ta Fastuma tana zama abin sha’awa ga al’umma, musamman lura da halin matsalar tsaro da wasu yankunan kasa ke ciki.

 

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.

Shugaban marasa rinjaye na Majalisar Wakilai Ali Isah, ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai na Majalisar bayan wata ganawa da mai kula da jihar Ribas Sole a Abuja.

 

Ali Isah, ya bayyana cewa mai kula da jihar ta Ribas ya kasance a gidan a wani bangare na ziyarar da ya saba yi domin yiwa kwamitin riko da ke sa ido kan al’amuran gwamnati.

 

Shugaban marasa rinjaye wanda ya jagoranci taron a madadin shugaban kwamitin wanda ya zama shugaban masu rinjaye na majalisar Farfesa Julius Ihonvere, ya bayyana gamsuwa da kokarin da mai gudanarwa shi kadai yake yi na wanzar da zaman lafiya a jihar.

 

Ya ce mai kula da jihar ya tuntubi manyan masu ruwa da tsaki kan rikicin shugabancin jihar Ribas, shugabannin cibiyoyin addini da na gargajiya, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki don ganin an warware matsalar cikin ruwan sanyi domin ci gaban jihar.

 

Sai dai jami’in da ya gabata, ya umurci mai kula da shi kadai da ya tabbatar da cewa rikicin shugabancin jihar Ribas bai shafi biyan albashin ma’aikatan gwamnati da wadanda suka yi ritaya duk wata da fansho ba kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da majalisar dokokin kasar ke yin duk mai yiwuwa don tabbatar da mulkin dimokuradiyya a kasar nan.

 

Ali Isah, ya kuma tabbatar da cewa kwamitin wucin gadi zai ci gaba da tuntubar mai gudanarwa da bangaren zartarwa don hana tsawaita dakatarwar daga wa’adin watanni shida domin samun ci gaba.

 

COV: TSIBIRI

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawul
  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana