Ya je Maiduguri daga Legas a kan keke
Published: 3rd, February 2025 GMT
Wani mahayin keken hawa, Samuel Fastuma, ɗan asalin Jihar Benue, ya kammala balaguronsa a kan keken hawa daga Legas zuwa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno a cikin kwanaki 8 kacal.
A cewar Fastuma, ya fara wannan tafiya ce a ranar Lahadi 19 ga watan Janairu, 2025 bisa ƙudirinsa na nuna fatan alheri ga daukacin masu yaƙi da fatara da masu yaƙi da muggan ƙwayoyi da kuma neman hadtin kai da zaman lafiya a tsakanin al’ummar Nijeriya.
Da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan isar sa birnin na Maiduguri, Fastuma ya ce, ya fara wannan tafiya ce domin yi wa matasa fatan alheri da kuma yin kira da a zauna lafiya a tsakanin ’yan Nijeriya.
Fastuma ya ce, “ina so in sanar da matasa, cewa abubuwa za su daidaita a cikin kasar nan don haka a cigaba da sa rai a kan hakan.
“Na yi imani cewa, idan kuna da basira, ya kamata ku yi amfani da ita domin hakan kan iya haifar da abubuwa masu girma na ci gaba.
“Tafiyar da na yi ta tsawon kwana takwas, na hadu da kalubale da dama da suka hada da rashin kyawun hanyoyin mota a wasu yankunan.”
Fastuma ya ce, “akwai wasu wurare masu kalubale, musamman tsakanin Bida da Npai, inda titin ba shi da kyau sosai.
“Haka nan na kuma fuskanci wasu matsaloli na bin hanyar Kano zuwa Potiskum.”
Duk da wadannan kalubale Fastuma ya jajirce kuma ya samu nasarar isa Maiduguri a ranar 26 ga watan Janairu.
“Na sha jin labarin Jihar Borno, amma wannan shi ne karo na farko da na kawo ziyara,” in ji shi.
‘‘Tsaro a kan titin ya yi matukar tsauri, kuma ya zuwa yanzu, na gano Jihar Borno wuri ne mai dadin rayuwa.”
Tafiya ta ban mamaki irin ta Fastuma tana zama abin sha’awa ga al’umma, musamman lura da halin matsalar tsaro da wasu yankunan kasa ke ciki.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.