An Fara Bukukuwan Kwanaki Goma Na Cin Nasarar Juyin Juya Halin Musulinci A Iran
Published: 31st, January 2025 GMT
Al’ummar kasar Iran sun fara gudanar da bukukuwan cika shekaru 46 da juyin juya halin Musulunci na shekara ta 1979, wanda ya kawo karshen mulkin kama karya, wanda ya kai ga kafuwar Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Kamar kowace shekara, ana fara bukukuwan ne da karfe 9:33 na safe, na ranar 1 ga Fabrairu, 1979, ga jirgin saman Air France da ya dawo da Imam Khumaini gida daga gudun hijira na sama da shekaru 14 wanda ya kai ga kafa Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
A yayin bukukuwan al’ummar Iran suna halartar taruka daban-daban har zuwa zagayowar ranar 22 ga watan Bahman wato 10 ga watan Fabrairu, wato ranar tunawa da juyin juya halin Musulunci.
Juyin juya halin Musulunci ba wai kawai ya sake fasalin tsarin siyasar Iran ba ne, har ma ya sake fasalin matsayinsa na duniya, tare da kafa Jamhuriyar Musulunci a matsayin sabuwar hanyar samun ‘yancin kai daga wani yanki na gabas ko na yamma.
Ta hanyar kifar da gwamnatin sarki Shah Pahlavi shekaru 46 da suka gabata, al’ummar Iran sun kawo karshen mulkin shekaru 2,500 na sarauta tare da kafa wani sabon tsarin siyasa jamhuriya mai tushe bisa kimar Musulunci da dimokuradiyya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’in Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Iran Ta Cimma Matsayi A Yaki Kwanaki 12
Jami’in ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa; Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta cimma babban matsayi a yakin kwanaki 12
Ali Baqiri Kani mamba a majalisar tsare-tsaren a ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta cimma babban matsayi a yakin kwanaki 12 da aka kwashe ana gwabzawa da yahudawan sahayoniyya.
Baqiri ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi ta gidan talabijin a yammacin jiya Asabar cewa: Tabbas Iran ta cimma matsayi sosai a yakin kwanaki 12 da aka kwashe ana gwabzawa, yana mai jaddada muhimmancin diflomasiyya wajen tunkarar hare-haren da ake kai wa kasar, yana mai jaddada cewa: “Dole ne Iran ta mayar da martanin wuce gona da iri kan kasarta a fagen diplomasiyya zuwa wani lamari da duniya ta amince da shi.”
Har ila yau Baqeri Kani ya yi ishara da hadin kan kasa a matsayin mafi girman bayyanar da Iran ta taka rawa a wannan yaki yana mai cewa: Wannan hadin kai yana nuna irin gagarumin goyon bayan da jami’an diflomasiyyar Iran suka nuna.
Ya kara da cewa: Goyon bayan jama’a ga manufofi da matakan gwamnatin na iya taimakawa wajen cimma manufofin diflomasiyya. Har ila yau ya bayyana cewa: A halin da ake ciki yanzu, kasashen yammacin duniya, baya ga Amurka, sun taka rawa wajen tallafawa hare-haren da aka kai wa Iran.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Jami’an Tsaron Iran Sun Murkushe ‘Yan Ta’adda Kan Ofishin ‘Yan Sanda A Kudu Maso Gabashin Kasar August 10, 2025 Jefa Agajin Abinci Ta Sama A Zirin Gaza Ya Janyo Shahadan Falasdinawa 23 Tare Da Jikkata Wasu 124 August 10, 2025 Tehran Times: Mai Yiwuwa Iran da Amurka su koma Tattaunawa August 10, 2025 Tel Aviv: Dubban yahudawa sun yi zanga-zangar adawa da yakin Gaza August 10, 2025 Welayati: Makircin Amurka da Isra’ila na kwance damarar Hizbullah ba zai yi nasara ba August 10, 2025 Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu August 10, 2025 Venezuela: An dakile yunkurin kai wasu munanan hare-hare a cikin kasar August 10, 2025 Pezeshkiyan Ya Yabawa Yan Jarida A Ayyukansu A Yakin Kwanaki 12 August 9, 2025 Yansanda A Burtaniya Ta kama Mutane Fiye Da 200 Masu Goyon Bayan Falasdinawa August 9, 2025 Iran Ta Yi Maraba Da Sulhuntawa Tsakanin Armenia Da Azerbaijan August 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci