MDD: Yaran Gaza 2,500 na fuskantar mutuwa matukar ba a yi gaggawar kwashe marasa lafiya ba
Published: 31st, January 2025 GMT
Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya yi kira da a gaggauta kwashe yara 2,500 da suka jikkata a yakin da Isra’ila ta kwashe watanni 15 tana yi a Gaza domin samun kulawar gaggawa.
Rokon nasa ya biyo bayan ganawar da ya yi da likitocin Amurka ne wadanda suka yi gargadin cewa yaran na fuskantar barazanar mutuwa a makonni masu zuwa.
Likitocin hudu, wadanda suka yi aikin sa kai a Gaza sun bayyana mummunan halin da yanayin kiwon lafiyar yankin ke ciki, wanda yakin ya yi wa illa.
Guterres ya ce ya ji dadin matuka bayan tattaunawarsa da likitocin Amurka ranar Alhamis. Ya kuma”Dole ne a kwashe yara 2,500 ba tare da bata lokaci ba, tare da ba da tabbacin cewa za su iya komawa ga iyalansu bayan sun samu lafiya, kamar yadda ya rubuta a shafukan sada zumunta.
Kwanaki kadan kafin a fara tsagaita wuta a ranar 19 ga watan Janairu, Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ba da rahoton cewa sama da Falasdinawa 12,000 ne ke jiran kulawar likitoci, kuma ana zaton cewa za a samu karuwar masu bukatar irin kulawa bayan tsagaita bude wuta.
Daga cikin wadanda ke bukatar agajin gaggawa akwai yara 2,500, a cewar Feroze Sidhwa, wani likitan tiyata daga California wanda ya yi aiki a Gaza daga ranar 25 ga Maris zuwa 8 ga Afrilun bara.
Bayanin ya ce daga cikin yaran 2,500 wasu sun fara mutuwa, kuma za su ci gaba da mutuwa matukar ba a gagaguta dake sub a a cewar Guterres.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49
Jami’in tafiyar da sha’anin Mulki a yankin Cape ya fada a jiya Laraba cewa; An sami karuwar wadanda su ka rasa rayukansu ya karu zuwa 49.
Shugaban tafiyar da sha’anin Mulki a yankin na garin Cape, Oscar Mobyan ya bayyana haka ne a wani taron manema labaru,kamar yadda kamfanin dillancin labarun Reuters ya nakalto.
Wasu yankuna na kasar ta Afirka Ta Kudu sun fuskanci saukar ruwa kamar da bakin kwarya, haka nan kuma saukar kankara, da hakan ya sa aka shiga cikin yanayin sanyi mai tsanani da kuma yankewar wutar lantarki a wasu yankunan.
Ambaliyar ruwan da aka samu a kusa da wata makaranta ya ja motar da take dauke da dalibai 13, da hakan ya yi sanadiyyar rasuwarsu. Tuni an tsamo gawawwakin dalibai shida,ana kuma ci gaba da neman sauran.
Sauyin yanayin duniya yaa shafi kasar Afirka Ta Kudu, ta yadda a cikin shekarun bayan nan ake yawan samu ambaliyar ruwa. A watan Aprilu na 2022 an yi mamakon ruwa guguwa mai karfi wacce ta ci rayukan kusan mutane 400.