Aminiya:
2025-10-13@13:37:48 GMT

Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku

Published: 13th, October 2025 GMT

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan yadda shugaba Bola Tinubu ya yi wa wasu mutane afuwa, ciki har da waɗanda suka aikata manyan laifuka.

A cikin saƙon da Atiku ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ana yin afuwa ne ga waɗanda aka yi wa rashin adalci ko waɗanda suka nema gafara bayan sun shafe wani lokaci a gidan yari.

Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna

Ya ce a wannan karon an yi wa masu safarar ƙwayoyi, masu garkuwa da mutane, masu kisan kai, da kuma masu cin hanci da rashawa afuwa.

Atiku, ya ce abin mamaki ne yadda gwamnati ke yafewa irin waɗannan mutane, a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsaro da lalacewar tarbiyya, musamman tsakanin matasa masu shan miyagun ƙwayoyi.

Ya ce bincike ya nuna cewa kashi 29 na waɗanda aka yi wa afuwa suna da alaƙa da hakrar miyagun ƙwayoyi, yayin da Najeriya ke ƙoƙarin wanke sunanta a idon duniya kan yaƙi da miyagun ƙwayoyi.

Atiku, ya ce maimakon wannan afuwa ta zama darasi ga masu laifi, ta zama hanyar durƙusa da ɓangaren shari’a da jami’an tsaro da ke sadaukar da rayukansu wajen kamawa da hukunta masu aikata laifuka.

Ya ƙara da cewa idan gwamnati ta fara yafe wa masu laifi, hakan zai rage ƙimar shugabanci kuma ya ƙarfafa wa masu aikata laifuka su ci gaba da aikata su.

Atiku ya jaddada cewa Najeriya tana buƙatar  shugabanci na gari wanda zai tabbatar da adalci a shari’a, ba tare da nuna bambanci ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Afuwa Miyagun ƙwayoyi Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta

Majiyar asbitoci a yankin gaza na kasar Falasdinu da aka mamaye ta bada labarin cewa HKI ta kashe falasdinawa 19 a safiyar yau Asabar duk tare da cewa an fara tsagaita budewa juna wuta a yankin.

Tashar talabian ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar asbitoci a gaza na cewa bayan janyewar sojojin HKI daga wasu yankuna a Gazar sun zakulo gawakin falasdinawa 155 daga burbushin gine-gine wadanda HKI ta rusa a bayan.

Banda haka an kawo masu sabbin gawaki 19 wadanda sojojin HKI suka kashe a safiyar yau duk tare da cewa an fara yarjeniyar dakatar da budewa juna wuta.

Labarin ya kara da cewa gawaki 135 daga cikin 155 da aka kawo na kashe-kashen baya ne. Labarin ya kara da cewa an kashe mutane 16 a lokacinda wani jirgin yakin HKI ya kai hari kanwani gida a Khan Yunus a safiyar yau Asabar. Wadanda suka mutun dangi guda ne.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Tana Goyon Bayan Duk Wani Shirin Zaman Lafiya Da Ya Hada Da Kawo Karshen Kisan Kiyashi A Gaza October 11, 2025 Faransa Da Jamus Da Kuma Birtaniya Sun Bayyana Aniyarsu Ta Ganin An Farfado Da Tattauna Da Iran October 11, 2025 Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza October 11, 2025 Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya October 11, 2025 Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta October 11, 2025 Putin: Natanyahu Yana Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba October 10, 2025 Majalisar Turai Ta Bukaci Kasashen Nahiyar Su Kakkabo Jiragen Yakin Rasha October 10, 2025 Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa October 10, 2025 Falasdinawa Daga Kudancin Gaza Sun Fara Komawa Gidajensu Da Aka  Rusa A Arewacin Yankin October 10, 2025 Rahotanni : Isra’ila ta fara janye dawa wasu yankuna na Gaza October 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
  • Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
  • HKI Ta Kashe Mutane 19 A Gaza Duk Tare Da Tsagaita Wuta
  • Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da Katsina
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano