Aminiya:
2025-11-27@21:16:04 GMT

Masarautar Nafada ta ƙaddamar da dokar rage tsadar aure

Published: 9th, October 2025 GMT

Mai Martaba Sarkin Nafada, Alhaji Dadum Hamza ya ƙaddamar da sabuwar doka ta rage tsadar aure a masarautarsa, a Jihar Gombe domin sauƙaƙa wa matasa yin aure da kuma magance matsalolin da ke hana sauƙin yin aure a cikin al’umma.

Wakilin Sarkin, Alhaji Umaru Muhammad Baraya (Madakin Nafada), ne ya gabatar da dokar yayin taron ƙaddamarwa da aka gudanar a Unguwar Madaki da ke Nafada ta Tsakiya, tare da halartar jami’an gwamnati, Alƙalan kotun majistare da jami’an tsaro.

’Yan sanda sun kama waɗanda ake zargi da kashe ma’aikaciyar Arise TV a Abuja Najeriya ta tafka asarar tiriliyan 14.5 sakamakon rikicin Boko Haram – UNICEF

Dokar za ta fara aiki daga wannan shekara ta 2025, inda aka gargaɗi matasa da su guji yin habaici ko izgili ga ma’aurata da kalmomin da ke nuna raini kamar: “Aure ya yi arha”. Duk wanda aka kama yana aikata hakan zai fuskanci hukunci.

Sarkin ya ce, matakin yana da nufin ƙarfafa tarbiyya, inganta zaman lafiya da haɗin kai a cikin al’umma, tare da rage nauyin da iyaye da matasa ke ɗauka wajen yin aure.

Ya ƙara da cewa, manufar dokar ita ce dawo da aure ya zama da sauƙi kamar yadda addini ya tanada.

Mahalarta taron sun yaba da wannan mataki, suna mai cewa zai taimaka wajen rage zaman banza da matsalolin da ke addabar matasa da iyalai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mai Martaba Sarkin Nafada

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro da ta addabi dukkan sassa a Nijeriya.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin wannan Larabar mai ɗauke da sa hannunsa, Tinubu ya bayyana cewa dole ne a ɗauki matakan gaggawa da suka dace domin fuskantar barazanar tsaro da ke ƙaruwa ƙasar nan.

Shugaban ya bayar da umarnin ɗaukar ƙarin jami’an tsaro da suka haɗa da jami’an ’yan sanda 20,000, lamarin da zai ƙara adadin jami’an zuwa 50,000.

Haka kuma, Tinubu ya bai wa rundunar sojin ƙasa da sauran hukumomin tsaro umarnin ɗaukar ƙarin jami’ai.

Sanarwar ta ce za a yi amfani da sansanonin masu yi wa ƙasa hidima NYSC a matsayin wuraren horas da sabbin ’yan sandan.

Ƙarin bayani na tafe…

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe
  • Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Tsirin Trump Na Zaman Lafiya