Babban Kwamandan IRGC Ya Jaddada Batun Wurga Makiya Cikin Mummunar Nadama
Published: 9th, October 2025 GMT
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci ya jaddada cewa: Duk wani kuskuren da makiya za su yi, za su fuskanci martani mai tsanani
Babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) Manjo Janar Mohammad Pakpour ya jaddada cewa: Duk wani kuskuren da makiya za su yi a mashigar tekun Farisa, da mashigar Hormuz da tsibirin Iran, za su fuskanci hukunci mai tsauri, nan take, murkushewa, da kuma nadama.
A cikin sakon taya murnar zagayowar ranar sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci, Manjo Janar Pakpour ya bayyana cewa: “A jajibirin ranar sojojin ruwa na dakarun kare juyin juya halin Musulunci, yana mika sakon taya murna ga babban matsayi na kwamandoji da mayakan da suka yi shahada a lokacin tsaro mai alfarma ta shekara (1980-1988), musamman jaruman dawwama a ranar 16 ga watan Maris ta shekara (1980-1988) a Tekun Fasha da suka hada da -Shahidai Nader Mahdavi, Bijan Kurd, Nasrallah Shafi’i, Gholam Hossein Tavasoli, Mehdi Mohammadiha, Khodadad Absalan, da Majid Mubaraki—waɗanda a cikin yaƙin jarumtaka, suka wargaza girman kan duniya kuma suka mayar da Tekun Fasha tamkar makabarta ga ’yan ta’adda.
Ya kara da cewa: Wannan babbar rana wata alama ce ta tabbatacciyar imani, da gwagwarmayar kaifin basira, da kuma jaddada karfin jarumai masu kishi na sojojin ruwa masu karfi na dakarun kare juyin juya halin Musulunci, wadanda ta hanyar bin umarnin babban kwamandan sojojin kasar (Allah ya kara masa yarda), suka kasance ma’abuta tutar tabbatar da tsaro na dindindin a yankin tekun Farisa, da mashigar Hormuz da mashigar tekun take kewaye da Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas: An Cimma Yarjejeniyar Karshen Kan Dakatar Da Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Gaza October 9, 2025 Kungiyar Jihadul-Islami Ta JInjinawa Al’ummar Falasdinu Kan Juriyarsu A Lokacin Yaki October 9, 2025 Shugaban Kasar Ecuador Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Kisan Gilla October 9, 2025 Venuzuwela Ta Kaddamar Da Atisayan Soji Don Mayar Da Martani Ga Barazanar Amuka October 9, 2025 Ronaldo Ya Zama Biloniya Na Farko Tsakanin Yan Kwallon Kafa A Duniya. October 9, 2025 Trump Ya ce An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Yakin Gaza October 9, 2025 M D D Ta yi Kira Da A Kawo Karshen Yakin Gaza Da Aka Kwashe Shekaru 2 Ana Yi. October 9, 2025 Iran da Rasha Sun Tattauna Kan Yadda Za su Inganta Yin Aiki Tare A Bangaren Nukiliya. October 9, 2025 Natanyahu Ya Ce Makamai Masu Linzami Masu Keta Nahiyoyi Na Iran Barazana Ce Ga Amurka October 8, 2025 Iran Da Sauran Kasashe Na Bakin Tekun Caspian Sun Rattaba Hannu Kan Yarjeniyar Tsaron Tekun October 8, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: dakarun kare juyin juya halin Musulunci
এছাড়াও পড়ুন:
Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda yake ziyarar aiki a kasar Oman ya gana da manzon musamman na MDD a kasar Yemen Hans Grundberg a jiya Litinin ya yi tir da yadda Haramtacciyar Kasar Isra’ila take keta dokoki tana kai wa kasashen wannan yankin hare-hare.
Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Iran ya kuma nuna kin amincewar jamhuyriyar musulunci ta Iran da yadda ake ci gaba da killace kasar Yemen, yana mai yin gargadi akan sakamakon da zai biyo bayan keta doka da ‘yan Sahayoniya suke yi da shi ne ci gaba da hargitsi da fadace-fadace a wannan yankin.
A nashi gefen manzon musamman na MDD a kasar Yemen ya bukaci ganin Iran ta ci gaba da bai wa Majalisar Dinkin Duniyar hadin kai domin kyautata rayuwar al’ummar kasar ta Yemen da kuma shimfida zaman lafiya.
A wani labari mai alaka da ma’aikatar harkokin wajen Iran ta amabci cewa za a yi ganawa a tsakanin minista Abbas Arakci da takwaransa na Faransa Jean Noel Baro a gobe Laraba 26/ Nuwamba a birnin Paris.
Jigon tattaunawar shi ne bunkasa alaka a tsakanin kasashen biyu da kuma batun furusunonin Faransa da suke a Iran.
Haka nan kuma tattaunawar bangarorin biyu za ta tabo halin da ake ciki a wannan yankin na yammacin Asiya, sai kuma Shirin Iran na makamashin Nukiliya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci