Falasdinawa na murna da tsagaita wutar hare-haren Isra’ila a Gaza
Published: 9th, October 2025 GMT
Falasdinawan da ke Gaza da Isra’ila ta shafe sama da shekara biyu tana kai wa hare-hare sun nuna jin dadi da farin ciki bayan sanar da yarjejeniyar tsagaita wuta da nufin kawo karshen yakin.
Yayinda labarin yarjejeniyar ya yadu a cikin yankin da aka kewaye, mazauna Khan Younis a kudancin Gaza sun fito tituna suna murna da fatan wannan zai zama farko zaman lafiya daga hare-haren Isra’ila.
“Alhamdulillah da wannan dakatar da fada, karshen zubar da jini da kashe-kashe… duk Gaza na cikin farin ciki,” in ji Abdul Majeed Abd Rabbo, mazaunin Gaza.
Yarjejeniyar tsagaita wutar, wadda Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da ita a daren Laraba, na nuni da mataki na farko na shirin kawo karshen yakin da ya dauki shekaru biyu.
Yarjejeniyar na bukatar sakin fursunonin Isra’ila da ke hannun Falasdinawa a Gaza a madadin sakin Falasdinawa da ke hannun Isra’ila, yayin da dakarun Isra’ila za su ja da baya zuwa “layin da aka amince da shi,” a cewar Trump.
“Wannan lokaci ne da ake dauka a matsayin na tarihi, wanda Falasdinawa suka dade suna jira,” in ji Khaled Shaat, wani mazaunin Gaza.
“Farin cikin da muka fara gani a tituna alama ce ta samun sauki daga kisan kiyashi da kashe-kashe.”
Gidan talabijin na Al Jazeera ya ce akwai alamun sauki ga jama’ar Gaza gaba daya. “Wannan lokaci ne na tarihi,” in ji shi.
Bayan fama da yunwa da Isra’ila ta jawo a yankin tsawon watanni, hankalin kowa ya koma kan lokacin da za a fara raba taimako, abinci da magunguna a matakin da aka gani a lokacin dakatar da fada na baya.
A daren Laraba dai, a karon farko Falasdinawa sun yi barci mai natsuwa da ba a saba da shi ba, yayin da hare-haren sama da suka zama ruwan dare suka ragu sosai.
Sai dai duk da haka, hukumar kare rayuka ta Gaza ta sanar da da Isra’ila ta kai musu wasu hare-hare bayan sanar da yarjejeniyar, ciki har da “jerin munanan hare-hare” a birnin Gaza.
Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce zai kira gwamnatinsa a ranar Alhamis don amincewa da mataki na farko na yarjejeniyar, yana mai cewa wannan rana ce mai girma ga Isra’ila.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Falasdinawa Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
Ministan harkokin wajen na Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Arakci wanda yake ziyarar aiki a kasar Oman ya gana da manzon musamman na MDD a kasar Yemen Hans Grundberg a jiya Litinin ya yi tir da yadda Haramtacciyar Kasar Isra’ila take keta dokoki tana kai wa kasashen wannan yankin hare-hare.
Haka nan kuma ministan harkokin wajen na Iran ya kuma nuna kin amincewar jamhuyriyar musulunci ta Iran da yadda ake ci gaba da killace kasar Yemen, yana mai yin gargadi akan sakamakon da zai biyo bayan keta doka da ‘yan Sahayoniya suke yi da shi ne ci gaba da hargitsi da fadace-fadace a wannan yankin.
A nashi gefen manzon musamman na MDD a kasar Yemen ya bukaci ganin Iran ta ci gaba da bai wa Majalisar Dinkin Duniyar hadin kai domin kyautata rayuwar al’ummar kasar ta Yemen da kuma shimfida zaman lafiya.
A wani labari mai alaka da ma’aikatar harkokin wajen Iran ta amabci cewa za a yi ganawa a tsakanin minista Abbas Arakci da takwaransa na Faransa Jean Noel Baro a gobe Laraba 26/ Nuwamba a birnin Paris.
Jigon tattaunawar shi ne bunkasa alaka a tsakanin kasashen biyu da kuma batun furusunonin Faransa da suke a Iran.
Haka nan kuma tattaunawar bangarorin biyu za ta tabo halin da ake ciki a wannan yankin na yammacin Asiya, sai kuma Shirin Iran na makamashin Nukiliya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci