’Yan sanda sun kama ɗan bindiga a kan iyakar Najeriya da Kamaru
Published: 8th, October 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wani mutum da ake zargin ɗan bindiga ne da ke aiki tsakanin iyakar Najeriya da Kamaru.
Rundunar ta kuma ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu, harsasai 80 da wasu tarin makamai.
Gwamnatin Gombe ta kafa hukumar bunkasa fasahar zamani da tattalin arziƙi Yadda Obasanjo ya ƙaddamar da cibiyar taron ƙasa da ƙasa a BauchiKakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa wanda aka kama, Adamu Adamu, mai shekaru 30, ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Song a Jihar Adamawa.
Amma wanda aka kama mazaunin unguwar Jauro Jatau da ke Akko, Jihar Gombe.
An kama shi ne ranar 4 ga watan Oktoba, 2025, bayan samun sahihan bayanai da suka nuna cewa yana tare da wata ƙungiyar masu garkuwa da mutane da ke aiki a tsakanin Najeriya da Kamaru.
A yayin wani samame da CSP Ali Madaki ya jagoranta a ƙarƙashin Operation Hattara, rundunar ta gano inda suka ɓoye makamai a wani tsauni da ke kusa da ƙauyen Wuro Biriji a Jihar Adamawa.
Rundunar ta ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biy, harsasai 80, gidan harsasai bakwai, sarƙoƙi, makulli, wuƙa da ƙananan jakunkuna huɗu.
Kwamishinan ’yan sandan Jihar, CP Bello Yahaya, ya yaba wa jami’in wajen kama wanda ake zargin.
Ya kuma jaddada ƙudirin rundunar na ci gaba da yaƙi da masu garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka.
Ya buƙaci jama’a su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro bayanai domin tabbatar da zaman lafiya a Gombe da sauran maƙwabtan jihohi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ɗan Bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
Wata kungiya mai zaman kanta ta tantance mutane 60 wadanda za’a yiwa aikin ido kyauta a wasu kananan hukumomi 2 dake jihar Jigawa.
Shugaban kungiyar mai zaman kanta, Alhaji Umar Saidu Yelleman Jambola ya bayyana cewar za’a gudanar da aikin ne kyauta ga mutane 60 a kananan hukumomin Malam madori da kaugama.
A cewar sa wadanda za su ci moriyar aikin an zabi su ne daga dukkanin mazabu da ke kananan hukumomin.
Sa’idu Yalleman ya kara da cewa yara da manya ne za su amfana da aikin idon kyauta wanda kungiyar ta dau nauyi.
Da yake jawabi ga manema labarai, Dr Abubakar Adamu yace wadanda aka tantance kuma suke da yanar ido za’a kai su asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano dake birnin Kano don yi masu aikin.
Wakilan shirin na kananan hukumomin Malam Madori and Kaugama, Malam Bashari Suleiman da Dan-Alhaji sun ce a mako mai zuwa ne za’a gudanar da aikin ga wadanda aka tantance.
Da yake jawabi a madadin wadanda zasu ci moriyar aikin, wakilan mazabun Garun-Gabas da Mairakumi, Mustapha Bala da Suraja Garba sun yabawa kokarin Alhaji Umar Jambola.
A nasu jawaban, Shugabannin kananan hukumomin Kaugama da Malam madori, Alhaji Salisu Sani Garun-Gabas da Alhaji Masaki Usman Dansule sun yaba da hobbasan Umar Jambola na taimakawa masu karamin karfi a kananan hukumominsu.
Usman Mohammed Zaria