Sashen Dauko Rahotanni Na NUJ Ya Sami Sabbin Shugabbanni A Nasarawa
Published: 7th, October 2025 GMT
Mambobin kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya NUJ reshen jihar Nasarawa sun zabi sabbin jami’anta da za su gudanar da harkokin kungiyar na tsawon shekaru uku masu zuwa.
Shugaban kwamitin zaben, Mista Samson Osuo, ya sanar da Abubakar Abdullahi na jaridar Daily Trust a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 21 da Danjuma Joseph na National Accord da kuri’u 9 a matsayin shugaban kungiyar.
Ya kuma bayyana cewa Mista Chris Nyamtu na gidan rediyon Najeriya ne ya yi nasara da kuri’u 21 yayin da Augustine Kuza na jaridar Pilot na Najeriya ya samu kuri’u 9 a matsayin Sakatare.
Mista Abel Daniel na jaridar Guardian a matsayin mataimakin shugaba
Awayi Kuje na NAN a matsayin Mataimakin Sakatare, Michael David na Daily Independent a matsayin Sakataren Kudi.
Wasu kuma. Collins Agwam na jaridar Punch a matsayin Ma’aji da Aliyu Muraki na Rediyon Najeriya Kaduna a matsayin mai bincike.
Ya kuma yabawa ’yan kungiyar bisa yadda suka kammala zaben sannan Shugaban NUJ na Jihar Nasarawa, Salihu Alkali, ya yaba wa shugaban kungiyar da ya da wa’adinsa ya kare, Mista Isaac Ukpoju bisa yadda aka samar da hadin kai, zaman lafiya da kuma tabbatar da zaman lafiya
Ya kuma bukaci ’yan uwa su ci gaba da bin ka’idojin sana’arsu, yana mai cewa ba zai amince da duk wani aiki na rarraba kan jama’a ba.
Aliyu Muraki/Lafia.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: NUJ Nasarawa
এছাড়াও পড়ুন:
Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
Sanarwar ta kara da cewa, “mun yi farin cikin ganin cewar yan wasan kungiyoyin biyu da jami’an wasan duk sun bar filin wasan ba tare da samun wani rauni ba kuma jami’an tsaro suka yi musu rakiya, kungiyar ta kara da cewa an kama wasu da dama da ake zargi da hannu a rikicin tare da mika su ga hukumomin tsaro domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.
Kungiyar ta jaddada kudirinta na tabbatar da zaman lafiya da da’a, kungiyar ta jaddada cewa za ta ci gaba da tabbatar da ingancin wasan kamar yadda hukumar NPFL da hukumar kwallon kafar Najeriya NFF ta tanada, Pillars ta kuma yi kira ga magoya bayanta da su gudanar da ayyukansu cikin lumana tare da ci gaba da ba kungiyar goyon baya, amma kuma wani bidiyo dake yawo a kafafen sada zumunta ya nuna yan wasan 3SC da aka jikkata tareda raunuka a jikinsu.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA