Sashen Dauko Rahotanni Na NUJ Ya Sami Sabbin Shugabbanni A Nasarawa
Published: 7th, October 2025 GMT
Mambobin kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya NUJ reshen jihar Nasarawa sun zabi sabbin jami’anta da za su gudanar da harkokin kungiyar na tsawon shekaru uku masu zuwa.
Shugaban kwamitin zaben, Mista Samson Osuo, ya sanar da Abubakar Abdullahi na jaridar Daily Trust a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 21 da Danjuma Joseph na National Accord da kuri’u 9 a matsayin shugaban kungiyar.
Ya kuma bayyana cewa Mista Chris Nyamtu na gidan rediyon Najeriya ne ya yi nasara da kuri’u 21 yayin da Augustine Kuza na jaridar Pilot na Najeriya ya samu kuri’u 9 a matsayin Sakatare.
Mista Abel Daniel na jaridar Guardian a matsayin mataimakin shugaba
Awayi Kuje na NAN a matsayin Mataimakin Sakatare, Michael David na Daily Independent a matsayin Sakataren Kudi.
Wasu kuma. Collins Agwam na jaridar Punch a matsayin Ma’aji da Aliyu Muraki na Rediyon Najeriya Kaduna a matsayin mai bincike.
Ya kuma yabawa ’yan kungiyar bisa yadda suka kammala zaben sannan Shugaban NUJ na Jihar Nasarawa, Salihu Alkali, ya yaba wa shugaban kungiyar da ya da wa’adinsa ya kare, Mista Isaac Ukpoju bisa yadda aka samar da hadin kai, zaman lafiya da kuma tabbatar da zaman lafiya
Ya kuma bukaci ’yan uwa su ci gaba da bin ka’idojin sana’arsu, yana mai cewa ba zai amince da duk wani aiki na rarraba kan jama’a ba.
Aliyu Muraki/Lafia.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: NUJ Nasarawa
এছাড়াও পড়ুন:
Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta sanar da cewa kasar a shirye take ta taimaka wa tarayyar Najeriya a fadan da take yi da ta’addanci.
Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Rasha Maria Zakharova ce ta bayyana hakan, sannan kuma ta jinjinawa kokarin da gwamnatin ta Najeriya take yi a wannan fagen na kalubalantar masu wuce gona da iri.
Zakharova ta kuma ce, matsayar Rasha ba ta sauya ba akan yadda take kallon ta’addanci a matsayin barazana ga zaman lafiya na duniya.
Haka nan kuma ta ce, Rasha a shirye take ta bayar da taimako da kuma aiki tare da kungiyoyin kasa da kasa da cibiyoyin MDD da kuma tarayyar Afirka.
Dangane da Najeriya, Zakharova ta kara da cewa; Rasha a shirye take ta ci gaba da bai wa Najeriya taimako, kuma sojoji da jami’an tsaron kasar suna da kwarewa mai yawa da su ka samu a fagen fada da ta’addanci.”
Haka nan kuma ta yi ishara da yadda fararen hula da su ka hada mata da yara suke jin jiki matuka saboda ayyukan ta’addanci.
Kasar Najeriya dai tana fama da matsalolin tsaro daga kungiyoyin ta’addanci da su ka hada Bokoharam, Iswap da kuma barayin daji masu garkuwa da mutane.
A cikin kasa da mako daya an sace daliban makarantun arewacin kasar da dama, da hakan ya tilastawa mahukunta rufe makarantu a jihohi masu yawa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Palasdinawa Sun Karbi Gawawwakin Shahidai 15 Daga ‘Yan Mamaya November 27, 2025 Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon Dake Takawa Makiya Birki November 27, 2025 Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 An Zabi Iran A Cikin Majalisar Zartarwa Ta Hukumar Yaki Da Makamai Masu Guba Ta Duniya CWC November 27, 2025 HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan November 27, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza November 26, 2025 Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci