Jerin ministocin da zargin takardu ya tabaibaye su
Published: 7th, October 2025 GMT
A yayin Ministan Kimiyya, Fasaha da Ƙirƙire-ƙirƙire, Uche Nnaji, ke fuskantar matsin lamba bayan ya amsa a gaban kotu cewa Jami’ar Najeriya da ke Nsukka (UNN) ba ta taɓa ba shi takardar digiri ba, zargin sa da amfani da takardun bogi da kafar PREMIUM TIMES ta bankaɗo ya ƙara ƙarfi.
Fadar Shugaban Ƙasa ta ce za ta jira hukuncin kotu kafin ta ɗauki mataki kan batun Nnaji.
Wannan ya sanya Mista Nnaji cikin jerin wasu ministoci da suka fuskanci irin wannan tuhuma:
– Uche NnajiUche Nnaji, wanda Shugaba Bola Tinubu ya nada a watan Yuli 2023, ya gabatar da takardar digiri da kuma takardar kammala aikin NYSC a lokacin tantancewa. Amma jami’ar UNN da hukumar NYSC sun ce ba su da masaniya da takardun da aka gabatar.
Tinubu ya umarci NAHCON ta rage kuɗin aikin Hajjin 2026 Makiyaya sun kashe manomi a gonarsa a BornoShugaban jami’ar UNN, Farfesa Simon Ortuanya, ya tabbatar cewa an ɗauki Nnaji karatu a 1981 amma bai kammala ba.
NYSC ma ta ce takardar da Nnaji ke amfani da ita ba ta da tushe.
– Olubunmi Tunji-OjoMinistan Cikin Gida, an zarge shi da gabatar da takardar NYSC ta bogi.
Amma daga bisani NYSC ta ce takardarsa ta gaskiya ce, bayan an sake tura shi aikin a 2019.
– Stella Oduah:Taohuwar Ministar Sufurin Jiragen Sama, an zarge ta da ƙin kammala aikin NYSC a 1982.
A 2023, EFCC ta gurfanar da ita bisa zargin jabun takardu da bayanan ƙarya. Ta musanta zargin, kuma shari’ar na gaban kotu.
– Hannatu MusawaSaɓanin Nnaji da Olubumi da ake zargi da amfani da takardun bogi, da Stella Oduah da ke zargi da ƙin kammala aiki NYSC, qn yi zargin cewa Ministar Al’adu da Tattalin Arzikin Ƙirƙre-ƙirƙiye, tana cikin aikin NYSC lokacin da aka naɗa ta a 2023.
Ministar ta ci gaba da kare kanta cewa ba ta aikata laifi ba, kuma ta kammala aikin NYSC.
Kotun tarayya ta yi watsi da ƙarar da aka shigar, duk da tambayoyi da ke ci gaba da tasowa.
– Adebayo Shittu:Tsohon Ministan Sadarwa, Adebayo Shittu kuma, an zarge shi ne kan ƙin halartar aikin NYSC kasancewar ya kammala jami’a ne a lokacin da yake ɗan shekara 25.
Amma ya bayyana cewa zaɓen sa da aka yi a matsayin ɗan Majalisar Dokokin Jihar Oyo ya maye gurbin aikin, amma NYSC ta ce ba haka doka ta tanada ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adebayo Shittu Takardun bogi
এছাড়াও পড়ুন:
An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
Sufeto Janar na ’Yan sandan Nijeriya, Olukayode Egbetokun, ya sanar da cewa sun aiwatar da umarnin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu na janye dakarunsu daga gadin ɗaiɗaikun mutane da ake kira VIP.
IG Egbetokun ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai a yau Alhamis, yana mai cewa zuwa yanzu sun janye dakaru 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya.
Mbappe ya ci ƙwallaye 4 rigis a wasan Madrid da Olympiacos An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji“Wannan karon za mu aiwatar da umarnin da kyau saboda umarnin shugaban ƙasa ne,” in ji shi.
“Babu wani gwamna, ko minista, ko abokaina da za su kira su takura min saboda sun san cewa umarnin shugaban ƙasa ne. Ina kuma da tabbacin cewa ba za su uzzura wa kwamashinonin ’yan sanda ba ma.”
Ya ƙara da cewa za su tura jami’an da aka janye zuwa “wuraren da aka fi buƙatarsu, musamman a wannan lokaci mai muhimmanci.”
Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da aika ’yan sanda ga manyan mutane domin ba su tsaro na musamman, yana mai mayar da su zuwa aikin tsaro da ya shafi al’umma baki ɗaya.
Kazalila, a ranar Laraba, 26 ga watan Nuwamba ne Tinubun ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro a faɗin ƙasar, inda ya bayar da umarnin a ɗauki matakan gaggawa domin magance matsalolin tsaro da ƙasar ke fuskanta.
Shugaban ya ce a ɗauki sababbin ’yan sanda 20,000, ƙari a kan guda 30,000 da ya fara amincewa a ɗauk, wanda za a yi amfani da sansanonin horar da masu yi wa ƙasa hidima wajen horar da sababbin ’yan sandan da za a ɗauka.