Masana kimiyya na kasar Sin sun gano cewa, falalen dutsen cikin duniyar wata da ke yanki mai nisa ya fi tsananin sanyi fiye da na yanki na kusa. Sun bayyana hakan ne bayan yin nazari kan samfurin kasa na yankin mai nisa da na’urar binciken duniyar wata ta Chang’e-6 ta kasar Sin ta dauko daga can.

Wannan binciken ya bayar da shaida game da yanayin samuwar duwatsu da sinadaran da suka hadu suka zama kasa da albarkatunta domin gano bambancin yanayin zafi a tsakanin yankin wata na kusa da kuma na nesa, inda hakan ya bayar da muhimman bayanan da ake bukata don fayyace samuwar halittar wata.

Cibiyar binciken sinadaran Uranium na karkashin kasa ta Beijing, da Jami’ar Peking da Jami’ar Shandong ne suka gudanar da binciken, kuma aka wallafa a cikin mujallar nazarin kimiyyar dabi’ar halitta ta “Nature Geoscience”. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

ShareTweetSendShare Sulaiman

Related Daga Birnin Sin Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar 4 hours ago Daga Birnin Sin CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare 19 hours ago Daga Birnin Sin Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243 20 hours ago

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

Daga Sani Sulaiman

 

Gwamnan Jihar Taraba, Dr. Agbu Kefas, ya yi jimami kan rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya rasu a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamban 2025, yana da shekaru 102.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai bai wa gwamnan shawara na musamman kan Yada Labarai da Hulda da Jama’a, Mista Emmanuel Bello, ya sanyawa hannu.

Gwamnan ya ce rasuwar wannan babban malami babban rashi ne ga kasa, yana mai nuna cewa a wannan lokaci ne ake matuƙar bukatar irin gudummawar da yake bayarwa, duba da kalubalen da kasar ke fusfuskanta.

Ya kara da cewa marigayi Sheikh ya koyar da ilimi da zai ci gaba da jagorantar kasa kan batun zaman lafiya tsakanin addinai.

Haka kuma, Dr. Kefas ya yabawa halayen Sheikh Bauchi, wanda ya bayyana shi a matsayin mutum mai tawali’u, jin kai, da haƙuri.

Saboda haka, Gwamna Agbu Kefas ya yi kira ga jama’a da su yi koyi da jagorancin wannan fitaccen malami.

Ya ce al’ummar  kasa za su ci gaba da bin tsarin ladabi da tarbiyyar da marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya koyar.

A wani bangaren, Dr. Kefas ya ja hankalin  ‘yan Najeriya da  su ci gaba da kasancewa cikin zaman lafiya da juna ba tare da la’akari da addininsu ba.

Ya jaddada muhimmancin jurewa da girmama ra’ayin juna maimakon nacewa a kan namu ra’ayin, tare da tabbatar da aniyarsa ta ci gaba da hidima ga dukkan ‘yan Jihar Taraba bisa adalci ba tare da la’akari da addini ko kabilarsu ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra
  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sake kai hari a Kwara, sun sace mutum 11
  • China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makaamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan