BBNaija S10: Ban san yadda zan kashe N150m da na lashe ba — Imisi Eniola
Published: 6th, October 2025 GMT
Gwarzuwar gasr Big Brother Naija (BBNaija) ta wannan shekara, Imisi Eniola Ayanwalwe, ta ce ba ta san yadda za ta kashe Naira miliyan 150 da ta lashe a gasar ba.
Imisi Eniola Ayanwale ce ta zama gwarzuwar BBNaija da aka kammala a daren Lahadi ne bayan kwanaki 70 ana fafatawa mai cike da ce-ce-ku-ce da nishaɗi.
An sanar da sakamakon tare da karrama ta da kyaututtuka ne a babban bikin ƙarshe da Ebuka Obi-Uchendu ya gabatar, inda Imisi ta doke abokiyar takararta Dede a karshe.
Ta tafi da tsabar kuɗi Naira miliyan 80 a matsayin wani ɓangare na kayatattun Naira miliyan 150 da ta lashe a matsayin gwarzuwar BBNaija karo na 10.
A bana, masu shirya gasar sun canja tsarin yadda ake fitar da zakara, inda suka ce za a zabi gwarzon ne daga cikin mutum 10 na ƙarshe da suka rage a gidan, maimakon mutum biyun ƙarshe kamar yadda aka saba. Amma daga bisani gasar ta dawo yadda aka saba, aka bar Imisi da Dede a zagayen ƙarshe kafin a sanar da sakamakon.
’Yan bindiga sun kashe wani mutum sun sace hakimi a Kwara Zargin takardun bogi: Jami’ar Nsukka ba ta taɓa ba ni takardar digiri ba — MinistaBayan sanar da ita a matsayin zakara, Imisi ta bayyana farin ciki da godiya, tana mai cewa har yanzu bata tsara yadda za ta yi da kuɗin ba.
Ta ce, “A gaskiya ban shirya yadda zan yi da kuɗin ba tukuna. Zan fara neman shawarar kuɗi tukunna, domin ban taɓa rike irin waɗannan maƙudan kuɗaɗe ba.”
A zamanta na ƙarshe da Big Brother kafin kammala gasar, Imisi ta bayyana cewa ta koyi darussa da dama yayin zamanta a gidan, ciki har da juriya da sanin kanta.
Imisi ta shahara saboda halayenta na raha, annashuwa da tsage gaskiya da kuma yadda take warware saɓani cikin natsuwa, abin da ya jawo mata masoya da dama a shafukan sada zumunta.
Kafin sanar da sakamakon, masu kallo sun zaƙu suna jiran wanda zai zama zakara a bana, wanda yanzu Imisi ta shiga jerin fitattun zakarun baya kamar su Phyna, Mercy Eke, Laycon, Whitemoney, da Ilebaye.
An rufe gasar ta BBNaija kaka ta S10 da shagulgula, inda Imisi ta bar dandali cikin farin ciki da kyaututtuka da kuma tarihi da ba za a manta da shi ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwarzuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Shugabannin masana’antu sun kuma yi kira ga gwamnati da ta daidaita tattalin arziki, inganta saukin gudanar da harkokin kasuwanci, da aiwatar da shirye-shiryen tallafi ga masana’antu na cikin gida.
Bugu da kari, masana sun nuna cewa rikicin kudin waje da rashin daidaito a kimar musayar kudi su ne manyan matsaloli ga kamfanoni masu zaman kansu daga kasashen waje, inda kalubalen samun damar mayar da ribar kamfani zuwa kasashen waje da samun kudin waje ke rage amincewar masu zuba jari sosai kuma yana karfafa su su bar kasar.
Binciken da LEADERSHIP Sunday ta gudanar ya nuna cewa yanayin tattalin arzikin Nijeriya ya sha wahala tun daga shekarar 2020, inda wasu kamfanoni suka rufe ayyukansu, ko suka yi kaura, ko kuma suka rage yawan ayyukansu a kasar.
Ana danganta wannan yanayi da wahalhalun tattalin arziki, canje-canjen kimar kudi, da tsadar gudanar da ayyuka, wanda hakan ya haifar da asarar ayyukan yi da kuma rashin daidaiton tattalin arziki mai yawa.
Wasu daga cikin manyan kamfanonin da suka bar Nijeriya sun hada da Standard Biscuits Nigeria Limited, NASCO Fiber Product Limited, Union Trading Company Nigeria Plc, da Deli Foods Nigeria Limited.
Ficewar wadannan kamfanonin daga kasuwar Nijeriya ya samo asali ne daga tasirin rashin daidaiton tattalin arziki da sauran kalubalen gudanarwa.
Yawancin kamfanonin sun bayyana cewa matsalolin tattalin arziki masu tsanani, canje-canjen kimar kudi marasa tabbas, da hauhawar farashin gudanar da ayyuka su ne manyan dalilan da suka sa suka yanke wannan shawara.
“Nijeriya dole ne ta samar da tsarin da zai ja hankalin wadanda za su zuba jari a masana’antu, hakar ma’adanai, wadanda za su sarrafa albarkatun kasa da kayan albarkatun da ake da su, tare da tabbatar da ci gaban tattalin arziki mai hadin kai,” in ji shi.
Haka kuma, shugaban Kungiyar Masu Kananan Harkokin Kasuwanci na Nijeriya (ASBON), Dakta Femi Egbesola, ya bayyana cewa ficewar kamfanoni masu zaman kansu na kasashen waje ya shafi yawancin Kananan da Matsakaitan Harkokin Kasuwanci (SMEs) da kamfanoni na cikin gida da ke aiki a kasar, tare da karawa da cewa gwamnati dole ne ta dauki matakan gaggawa don hana ficewar kamfanonin ketare.
A yayin da yake magana da daya daga cikin wakilanmu, Daraktan Gudanarwa na Cowry Asset Management Company, Johnson Chukwu, ya bayyana cewa haduwar rikicin kudin waje da rashin daidaito a kimar musayar kudi ya yi tasiri mara kyau ga ra’ayin masu zuba jari na kasashen waje wajen ci gaba da shiga harkokin zuba jari na kamfanoni masu zaman kansu a kasar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA