Uwargidan Gwamnan Jihar Ribas, Eyoanwan Bassey Otu, ta ce aƙalla mata da ƙananan yara 95,000 ne ke mutuwa a kowace shekara a Najeriya sakamakon shaƙar hayaƙin girki.

Ta bayyana haka ne yayin wani taron wayar da kai da aka gudanar a ofishinta da ke Kalaba, inda ta jaddada buƙatar amfani da hanyoyin girki masu tsafta da aminci a Najeriya.

Wike ya gana da Fubara da dattawan Ribas kafin kafa sabuwar majalisar zartarwa Rundunar Sojin Nijeriya ta cafke jami’anta 16 kan saɓa ƙa’idar aiki

Uwargidan gwamnan, wacce Asi Akiba, matar ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Kalaba, Kalaba ta Kudu da Odukpani ta wakilta, ta ce hayaƙin itacen girki da sauran hanyoyin da ba su da inganci sun zama hanyar mutuwa ta uku mafi yawa a Najeriya, bayan zazzabin cizon sauro da cuta mai karya garkuwar jiki.

Ta kuma jaddada cewa amfani da itace wajen girki na lalata muhalli, domin hayaƙin yana sakin wani sinadari wanda ke haddasa ɗumamar yanayi.

A yayin taron, an raba tukwanen girki 200 don rage yawaitar hayaƙi, domin ƙarfafa wa mutane guiwa su koma amfani da hanyoyin girki masu tsafta.

Uwargida Otu, ta ce tukwanen suna rage yawan itacen da ake ƙonawa,  kuma rage hayaƙin da ke shafar lafiyar mata da yara.

Shi ma Mista Oden Ewa, shugaban Hukumar Green Economy Commission, ya yi magana a taron, inda ya ce miliyoyin gidaje a Najeriya har yanzu sun dogaro da itace wajen girki, wanda hakan ke haddasa cututtuka.

Ya bayyana cewar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), ta ce hayaƙin cikin gida na ɗaya daga cikin manyan dalilan mutuwa barkatai musamman a ƙasashe masu tasowa.

Wannan shiri, a cewarsa, na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na kare muhalli, rage hatsarin kamuwa da cuta, da kuma inganta amfani da fasahohin makamashi aNajeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fatakwal Hayaƙi Mutuwa Uwargidan Fubara

এছাড়াও পড়ুন:

Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako

Gidajen mai da dam aka rufe, yayin da wadanda suka kasance da dan sauran mai kuma, layuka ne marasa iyaka suka makare su, lamarin da ta kai har kwana mutane ke yi a gidajen man.

 

A kan titunan babban birnin kasar, bayanai sun ce ba kasafai ake ganin motoci suna kai komo ba, ko kuma mutane na tura babura, bisa alama dai mutane sun ajiye ababen hawansu a gida.

 

Sai dai duk da wannan karancin man da ake fama da shi, farashinsa ya ci gaba da kasancewa a yanda yake, domin kuwa farashin lita na mai CFA 775 yayin da dizal yake akan CFA 725.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba October 12, 2025 Manyan Labarai An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro October 12, 2025 Manyan Labarai Trump Da Al-Sisi Za Su Jagoranci Taron Zaman Lafiya Dawwamammiya Ta Gaza A Masar October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Tsokaci A Kan Mata Masu Tsananin Kishi
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
  • Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata
  • Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya