’Yan sanda sun bindige Lakurawa 3 har lahira a Kebbi
Published: 4th, October 2025 GMT
’Yan sanda sun harbe wasu mayaƙan Lakurawa har lahira a yayin da ragowar suka tsere a yankin Gorun Yamma da ke Ƙaramar Hukumar Dandi da ke Jihar Kebbi.
Kakakin rundunar, SP Nafi’u Abubakar , a cikin wata sanarwa a ranar Asabar ya ce bayan samun rahoton harin ’yan ta’addan a yankin ne ’yan sanda suka je suka yi musayar wuta na tsawon awannin da su, inda suka halaka mutum 3 a cikin maharan, ragowar kuma suka cika bujensu da iska.
Sanarwar da ya fitar a ranar Asabar ta ce bayan samun rahoto ne DPO na yankin Lamba ya tura ’yan sanda da ’yan banga domin fatattakar maharan,
Ya ce an ƙwace babur guda ɗaya da mayaƙan na Lakurawa suka tsere suka bari.
Ya ƙara da cewa Kwamishinan ’yan sandan jihar Bello M. Sani ya jinjina wa DPOn da dakarunsa bisa ɗaukar mataki cikin gaggawa.
Ya ƙara da kira a gare su da su ƙara zage dantse domin fatattakar Lakurawa da sauran ’yan ta’adda da masu laifi a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Lakurawa
এছাড়াও পড়ুন:
An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
An wallafa wasu kundi 2 masu kunshe da ra’ayoyin shugaba Xi Jinping na kasar Sin kan batutuwan da suka shafi mata da yara da kungiyar mata ta kasar, da kuma ra’ayoyinsa kan karfafa zumunci da akidu da al’adun iyali, cikin harsunan Rashanci da Faransanci da Spaniyanci da Larabci, bayan irinsu da aka wallafa cikin harsunan Ingilishi.
Madabba’ar tattara bayanai da fassara ta kwamitin tsakiyar JKS ce ta wallafa kundin, wadanda ake sa ran za su taimakawa masu karatu na kasa da kasa kara fahimtar ra’ayoyin shugaba Xi da dabaru da shawarwarin da Sin ta gabatar game da daukaka daidaiton jinsi da raya dukkan harkokin da suka shafi mata a fadin duniya. (Fa’iza Mustapha)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA