Aminiya:
2025-11-27@21:16:49 GMT

’Yan sanda sun bindige Lakurawa 3 har lahira a Kebbi

Published: 4th, October 2025 GMT

’Yan sanda sun harbe wasu mayaƙan Lakurawa har lahira a yayin da ragowar suka tsere a yankin Gorun Yamma da ke Ƙaramar Hukumar Dandi da ke Jihar Kebbi.

Kakakin rundunar, SP Nafi’u Abubakar , a cikin wata sanarwa a ranar Asabar ya ce bayan samun rahoton harin ’yan ta’addan a yankin ne ’yan sanda suka je suka yi musayar wuta na tsawon awannin da su, inda suka halaka mutum 3 a cikin maharan, ragowar kuma suka cika bujensu da iska.

Sanarwar da ya fitar a ranar Asabar ta ce bayan samun rahoto ne DPO na yankin Lamba ya tura ’yan sanda da ’yan banga domin fatattakar maharan,

Ya ce an ƙwace babur guda ɗaya da mayaƙan na Lakurawa suka tsere suka bari.

Ya ƙara da cewa Kwamishinan ’yan sandan jihar Bello M. Sani ya jinjina wa DPOn da dakarunsa bisa ɗaukar mataki cikin gaggawa.

Ya ƙara da kira a gare su da su ƙara zage dantse domin fatattakar Lakurawa da sauran ’yan ta’adda da masu laifi a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Lakurawa

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi

An ceto ’yan matan nan 24 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a Makarantar sakandaren Gwamnati ta GGCSS da ke yankin Maga da ke Jihar Kebbi.

Gwamnan jihar Kebbi Nasiru Idiris a taron manema labarai a ranar Talata fadar gwamnatin jihar ya tabbatar da an karɓo ɗalibban da aka sace a farkon makon nan.

Ya ce “an karɓo ɗiyanmu ’yan makaranta waɗanda aka yi garkuwa da su a Maga. Shugaban ƙasa ya baiwa jami’an tsaro umarni a tafi a gano inda yaran suke kuma a karɓo su muna tabbatar wa uwayen yara da al’ummar Kebbi yara sun dawo.

“Muna godiya ga shugaban ƙasa da jami’an tsaro musamman sojoji da ’yan sanda da Sibil difens da sauransu da suka tsaya aka karɓo yaran nan cikin ƙoshin lafiya.

“Mu gwamnatin Kebbi ba mu biya kuɗin fansa don a saki yaran ba, a binciken da muka yi ba wanda ya biya kuɗin fansar yaran, mu ba mu ba da ko kwabo ba,” a cewar Gwamnan Idiris.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • Juyin mulki ya rutsa da Jonathan a Guinea-Bissau
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin
  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe