Aminiya:
2025-11-27@21:14:36 GMT

Shekara 1 bayan rushewa, har yanzu ba gyara titin Kano–Maiduguri ba

Published: 29th, September 2025 GMT

Shekara guda matafiya da direbobi a ƙauyukan Malori-Guskuri da Sabon Gari da ke Ƙaramar Hukumar Katagum a Jihar Bauchi na ci gaba da fama da wahala bayan da ruwan sama ya karya babban titin Kano–Maiduguri.

A ranar 7 ga Agusta, 2024 ne ruwa ya cinye babbar hanyar a Malori-Guskuri, ya kuma yanke babban ɓangare na hanya.

Mako guda bayan nan kuma wani ɓangaren ya rushe a Sabon Gari.

Shekara guda da wata ɗaya bayan faruwar lamarin, wanda ya mayar wuraren da suka rushe sun koma tarkon mutuwa da ke haddasa haɗurra da suka kashe mutane da raunata wasu da dama.

Wakilinmu da ya kai ziyara ya samu wani kamfanin gine-gine ya dawo Malori da kayan aikinsa. Mazauna sun tabbatar da cewa a makon da ya gabata ne kamfanin ya dawo wurin—fiye da shekara guda bayan lalacewar hanyar.

Yajin aiki: Likitoci sun ba wa gwamnati wa’adin kwana 30 Ana zargin ’yan sanda da kashe limami a Kano

Duk da haka ɓangaren Sabon Gari bai samu gyara ba, lamarin da ke ci gaba da jefa direbobi da sauran matafiya da mazauna cikin hatsari.

Wani direban tifa kuma PRO na ƙungiyar direbobin tifa a Katagum, Shehu Muhammad, ya bayyana ɓangaren Sabon Gari a matsayin “tarkon mutuwa.”

“Wannan wurin ya zama tarko. Na shaida lokacin da motoci biyu cike da fasinjoji suka faɗa cikin wurin da ya yanke. Akwai lokaci da ake yi aikin ceto, aka fitar da wata mata ba ta da hayyacinta, sauran kuma sun samu munanan raunuka,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa duk da muhimmancin hanyar wajen haɗa manyan cibiyoyin kasuwanci a Arewacin Najeriya, gwamnati ta yi jinkiri wajen ɗaukar mataki.

“Mun gaji da jira. Abin takaici ne, muna da sanata da ’yan mambobin majalisar wakilai da shugaban ƙaramar hukuma, amma kamar ba sa bi ta wannan hanya. Muna roƙon Allah Ya taɓa zukatan shugabanni su kawo ɗauki,” in ji shi.

Shi ma wani direba mai suna Muhammadu Salisu, wanda aka fi sani da Salisu Mai Tifa, ya ce sama da shekara guda ke nan suna fama da wannan lalacewar hanyar, musamman a Sabon Gari.

Ya ce, “Wurin ya zama tarko. A farkon wannan shekara ruwan sama ya cinye hanyar gaba ɗaya. Mutane da dama sun mutu a haɗurra, dukiya kuma ta salwanta,” in ji shi.

Ya bayyana cewa akwai lokacin da hukumomi suka sa manyan injina suka toshe wani ɓangare na hanya don rage hadurra, amma daga bisani kamfanin ya ja da baya ya bar aikin.

A bangaren mazauna kuwa, Safiyanu Garba na Sabon Gari ya ce hadurra sun zama kusan kullum.

“Da wuya kwanaki 10 su wuce ba tare da an samu haɗari ba. Wasu lokutan masu babura da fasinjoji kan rasa rayukansu a wurin,” in ji shi.

Shi ma Muhammadu Dadi na Malori ya ce rushewar ta addabi jama’a musamman a lokacin damina, inda ruwan sama ke taruwa a rami ya toshe hanyar tafiya a ƙafa.

Yahaya Mohammed, wani mazaunin Malori, ya tabbatar da mutuwar mutane da dama a wurin, ya kuma ce sun ji daɗin ganin kamfanin ya dawo da injina don fara aikin gyaran.

Lokacin da aka tuntuɓi PRO na kamfanin Triacta, Ibrahim, ya ce sai ya tattauna da shugabanni kafin ya ba da bayani, amma bai samu damar yin hakan kafin lokacin bugawa ba.

Ƙoƙarin jin ta bakin Kwanturola na Ma’aikatar Ayyuka a Bauchi bai yi nasara ba. Sai dai wani jami’in ma’aikatar ya shaida wa wakilinmu a asirce cewa Gwamnatin Tarayya ta sake ba da kwangilar ne ga kamfanin Triacta.

A cewarsa, kamfanin ya fara da ɓangaren Malori ne saboda tsananin wahalar aikin, kafin ya koma Sabon Gari bayan kammala wannan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hanya Sabon Gari a Sabon Gari kamfanin ya

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa

Gwamnonin jihohin  Arewa 19 za su gudanar da muhimmin taro a ranar Asabar, 29 ga Nuwamba, domin tattauna matsalolin tsaro da suka addabi yankin.

Mai bai wa Gwamnan Nasarawa shawara na musamman kan harkokin jama’a, Peter Ahemba, ne ya sanar cewa, taron gwamnonin Arewa da aka shirya a Kaduna zai samu halartar manyan sarakunan gargajiya.

“Manufar taron ita ce samar da matsaya ɗaya wajen fuskantar matsalolin tsaro da ke damun yankin, tare da tsara hanyar magance su,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, za a yanke muhimman shawarwari a taron domin tabbatar da tsaron yankin.

’Yan Majalisar Kudu sun roƙi Tinubu ya yi wa Nnamdi Kanu Afuwa Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina

Ahemba ya bayyana cewa, sakamakon ƙalubalen tsaro da wasu jihohin Arewa ke fuskanta, gwamnatin Nasarawa ta ɗauki matakan gaggawa ta hanyar shirya taron tsaro na musamman, inda za a yanke shawarar da za ta kare jihar daga duk wata barazanar tsaro.

“Ya zama wajibi ga ’yan ƙasa su taka rawa wajen magance barazanar tsaro a ƙasarmu da jihohinmu. Don haka, dole ne jama’a su riƙa ba wa hukumomin tsaro bayanai kan mutanen da ke da halin aikata laifi,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • ’Yan sanda sun gano harsasai 210 a kan titin Zariya-Funtuwa
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila
  • Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa sun shirya taron gaggawa
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi