Aminiya:
2025-11-27@21:46:06 GMT

Me ya sa wasu ƙasashen Afirka ba sa goyon bayan kafa ƙasar Falasɗinu?

Published: 27th, September 2025 GMT

Yayin da ƙasashe irin su Birtaniya, Kanada da Ostareliya suka amince da kafa ƙasar Falasṭinu, ana tsammanin samun ƙarin wasu ƙasashe.

Shugaban Falasɗinu, Mahmud Abbas, ya yaba da wannan mataki tare da kira ga sauran ƙasashe su nuna irin wannan goyon baya.

Zargin ɓatanci: Kwamitin Shura na Kano ya fara sauraron koke-koke kan Malam Triumph An gano yarinya da aka sayar ₦3.

7m a Ondo

Yawancin ƙasashen Afirka sun riga sun amince da Falasdɗinu tun shekarun 1980.

Shugabanni irin su Thomas Sankara da Nelson Mandela sun taɓa danganta gwagwarmayar Falasɗinawa da irin ta Afirka na neman ’yanci.

Amma har yanzu akwai ƙasashe biyu da ba su amince da kafa ƙasar Falasɗinu ba; wato Kamaru da Eritrea.

Kamaru

Kamaru tana da alaƙa mai ƙarfi da Isra’ila musamman a fannin tsaro.

Isra’ila na bai wa dakarun Kamaru horo, tana kuma taimaka mata wajen tabbatar da tsaron gwamnatin ƙasar.

Wannan ya sa Kamaru ba ta son lalata alaƙarta da Isra’ila.

Haka kuma, gwamnatin na tsoron idan ta goyi bayan kafa Falasɗinu, masu fafutukar ɓallewar yankin Ambazonia a cikin ƙasar za su samu ƙarin hujja.

Saboda haka, Kamaru kan guji bayyana ra’ayinta kan kafa ƙasar Falasɗinu.

Eritrea

Eritrea kuwa ta samo matsayarta daga tarihi.

Lokacin da Falasɗinu ta nemi goyon bayan Afirka a shekarun 1980, shugabanta Yasser Arafat ya fi kusanci da Habasha wadda ke da alaƙa da Tarayyar Soviet, ba da Eritrea ba, alhali a lokacin Eritrea na fama da yaƙin neman ’yanci daga Habasha.

Wannan ya haifar da ɓacin rai a tsakanin ’yan Eritrea.

Duk da haka, Shugaban Eritrea Isaias Afwerki ya taɓa nuna tausayawa ga Falasɗinu, har ma ya amince da matsayin Falasɗinu a Majalisar Ɗinkin Duniya a 2012.

Amma bai yadda da tsarin “ƙasashe biyu” na yarjejeniyar Oslo ba, yana ganin ba zai kawo zaman lafiya ba.

Sai dai matsin lamba na cikin gida na iya taso masa, domin kusan rabin jama’ar Eritrea Musulmai ne.

A mahangar masana, hakan zai yi kama da rashin adalci idan ƙasar da ta yi nasarar samun ’yanci ba ta goyi bayan wasu su ma su samu ’yanci ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yanci Kamaru Ƙasa kafa ƙasar

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta

Sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran Dr Ali Larijan wanda ya ke ziyarar aiki na kwanaki uku a kasar Pakistan ya yabawa kasar saboda goyon bayan da ta bawa kasarsa a lokacin yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka dorawa kasar.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Dr Ali Larijana yana fadar haka a shafinsa na X a jiya Talata.  Sannan yace ya isar da sakon gaisuwa na Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khami’ae ga mutanen kasar Pakistan. Banda haka ya gana da Firai ministan kasar  Shehbaz Sharif da shugaban kasa Asif Ali Zardari da kuma kakakin majalisar dokokin kasar kasar Sardar Avaz Saadik.

A ganawar Larijani da Sharif sun tattauna kan dangantaka mai tsawo da ke tsakanin Iran da Pakisatan, da kuma bukatar a kara zurfafata.

Sharif a nasa bangaren ya bayyana cewa nan ba da dadewa waministan harkokin wajen kasar Mohammad Ishak Dar zai ziyarci Tehran inda ake saran zai rattaba hannu kan yarjeniyoyi na bunkasa tattalin arzikin kasashen biyu, daga ciki har da batun kammala aikin shimfida bututun gas  daga kasar Iran zuwa Pakistan. Da kuma harkokin sadarwa.

A cikin wannan shekarar ne dai kasashen biyu suka rattaba hannu kan yarjeniyar bunkasa kasuwanci ta dalar Amurka billion 10 a tsakaninsu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka EU da AU na taro kan diyya ga laifukan mulkin mallaka da cinikin bayi November 25, 2025 Hizbullah: Isra’ila na kure idan ta na tunanin kashe-kashe zai kawo karshen kungiyarmu November 25, 2025 Tashar Press TV ta kaddamar da sashen harshen Hebrew November 25, 2025 Bincike : Isra’ila Ta Kashe Falasdinawa Akalla 100,000 a Gaza November 25, 2025 Kasar Gambia Ta Bai Wa Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasar Kasar Kamaru  Mafaka Ta Wucin Gadi November 25, 2025 China Ta Yi Tir Da Yadda Kasar Japan Ta Girke Makamai Masu Linzami A Kusa Da Yankin Taiwan November 25, 2025 Velayati: Alakar Iran da Iraki tana da karfi November 25, 2025 Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin November 25, 2025 An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Tabarbarewar Tsaro na Barazana ga Siyasar Ƙasar Nan Gabanin Zaɓen 2027-Ado Doguwa
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yabawa Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • Shugaban Majalisar Koli Ta Taron Kasa Iran Ya Yawaba Pakistan Saboda Goyon Bayanta
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • NAJERIYA A YAU: Irin Radadin Da Masu Cutar Amosanin Jini Ke Fuskanta
  • Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi