Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (3)
Published: 26th, September 2025 GMT
Duk wani bangaren wayewa da kimiyya da fasaha za ka ga asali malaman Musulunci ne suka zo da shi, babu lokaci isasshe da mun kawo misalai masu yawa. yana daga cikin wayewar nan: tashi a sama zuwa duniyar wata, da duk “technology” din nan na zamani, harkar zane-zane, kade-kade, bushe-bushe. Amma duk aka kwashe wadannan aka bar mu sai dai halal da haram kawai! Su ma din an hana ma halal din gurbin ta, ba mu da wata magana sai dai haram! Da a ce malamai biyar za su taru, to za ka ga ba za su kago komai ba sai haram.
Jama’a mu waye, saboda addininmu wayayye ne, Annabinmu wayayye ne, Kur’aninmu wayayye ne. Abin da yasa bama fadar wadansu abubuwan ma saboda raunana. Amma yanzu an waye duka gaba daya, wayar salular nan taka babban malami ce, ka tambayi “Google” ko mene ne za ta zo maka da labarin komai, duk wasu abubuwa da aka canza a addinin nan siyasa ce ta jawo aka canza shi, amma asalinsa lafiya kalau yake, duk wayewa ce da sauki da ci gaba, idan ka duba Al-kur’ani duk haka za ka gani.
Mu yi murna dai jama’a, kuma yana ga kan malamai na addini, su rika binciken gaskiya duk inda take, su rika binciken ilimi, mu koma ma manyan littafai, littafan da aka yi tun daga wajen karni na biyu, abubuwa sun faru da yawa wanda ba za su fadu ba, amma ga littafai na karni na biyu tun daga nan aka fara, malamai sun yi kokari, mu rika koma ma wadannan da wayewa da fahimta da kwakwalwa irin ta zamani ba irin ta wancan zamani ba, saboda duk abin da suka yi mai kyau ne, amma kuma an ci gaba, Allah shi ne zamani, Allah ya kawo wayewa, Allah ya kawo wadanda Annabi da kansa ya fadi zuwan zamaninsu da wayewarsu. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce “Karshen zamani ilImi zai yawaita”. Amma ikon Allah, galibin littafan da muke karantawa suna nuni da karshen zamani ilimi zai kare. Ka san babu wanda ya isa ya ce ilimi ya kare a yanzu, yanzu ilmi ya fara ma! Ka ga ashe wannan hadisi da Manzon Allah ya ce karshen zamani ilimi zai yawaita gaskiya ne kuma shi ne daga Manzon Allah (SAW), ba littafan malaman nan ba.
Don Allah malamai ku duba manyan littafai, ku zama masu amana ta ilimi (amana ilmiyya), ku zamanto masu hango ma al’umma ci gaba, da wayewa, ba masu dakikantar da al’umma ba, ku zamanto jagorori a cikin duk abin da za ku fada, da duk abinda za ku rubuta, da duk littafin da za ku yi, duk abin da kuka yi zai same ku a cikin kabarinku. Kar don wani abu bai dace da jama’arku ba ku ce karya ne, ko ku ki yarda da shi, ko bai dace da kabilarku ba, ko bai dace da kungiyar da kake bi ba. Duk wadannan sun shiga cikin addini sun lalata shi, ba laifi rike akidu da maz’habobi amma kuma ya kamata a dauki abubuwan da suke ciki masu kyau a zubar da abubuwan da ba su da kyau. Zamani ya yi fa wanda in dai ba mu gyara ba Allah zai gyara mana fa! Manzon Allah (SAW) ya yi gaskiya, mai gaskiya ne abin gaskatawa, ya isar da sako kuma ya isar da amana. Mu zama masu adalci; asali shi ne wanda zai yi hukunci a tsakanina jama’a biyu kuma ya yi adalci a tsakaninsu. Kisdu kuma shi ne a tsakanin mutum biyu kawai, misali kamar tsakanin mai awo da wanda ake wa awon.
Muna taya dukkan al’ummar musulmi murnar ganin wannan lokaci mai tarihi na cikar Manzon Allah (SAW) shekara 1500 da haihuwa. Alhamdu Lillah!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Murnaz Haihuwaz Maulidi SAW
এছাড়াও পড়ুন:
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Shugabannin masana’antu sun kuma yi kira ga gwamnati da ta daidaita tattalin arziki, inganta saukin gudanar da harkokin kasuwanci, da aiwatar da shirye-shiryen tallafi ga masana’antu na cikin gida.
Bugu da kari, masana sun nuna cewa rikicin kudin waje da rashin daidaito a kimar musayar kudi su ne manyan matsaloli ga kamfanoni masu zaman kansu daga kasashen waje, inda kalubalen samun damar mayar da ribar kamfani zuwa kasashen waje da samun kudin waje ke rage amincewar masu zuba jari sosai kuma yana karfafa su su bar kasar.
Binciken da LEADERSHIP Sunday ta gudanar ya nuna cewa yanayin tattalin arzikin Nijeriya ya sha wahala tun daga shekarar 2020, inda wasu kamfanoni suka rufe ayyukansu, ko suka yi kaura, ko kuma suka rage yawan ayyukansu a kasar.
Ana danganta wannan yanayi da wahalhalun tattalin arziki, canje-canjen kimar kudi, da tsadar gudanar da ayyuka, wanda hakan ya haifar da asarar ayyukan yi da kuma rashin daidaiton tattalin arziki mai yawa.
Wasu daga cikin manyan kamfanonin da suka bar Nijeriya sun hada da Standard Biscuits Nigeria Limited, NASCO Fiber Product Limited, Union Trading Company Nigeria Plc, da Deli Foods Nigeria Limited.
Ficewar wadannan kamfanonin daga kasuwar Nijeriya ya samo asali ne daga tasirin rashin daidaiton tattalin arziki da sauran kalubalen gudanarwa.
Yawancin kamfanonin sun bayyana cewa matsalolin tattalin arziki masu tsanani, canje-canjen kimar kudi marasa tabbas, da hauhawar farashin gudanar da ayyuka su ne manyan dalilan da suka sa suka yanke wannan shawara.
“Nijeriya dole ne ta samar da tsarin da zai ja hankalin wadanda za su zuba jari a masana’antu, hakar ma’adanai, wadanda za su sarrafa albarkatun kasa da kayan albarkatun da ake da su, tare da tabbatar da ci gaban tattalin arziki mai hadin kai,” in ji shi.
Haka kuma, shugaban Kungiyar Masu Kananan Harkokin Kasuwanci na Nijeriya (ASBON), Dakta Femi Egbesola, ya bayyana cewa ficewar kamfanoni masu zaman kansu na kasashen waje ya shafi yawancin Kananan da Matsakaitan Harkokin Kasuwanci (SMEs) da kamfanoni na cikin gida da ke aiki a kasar, tare da karawa da cewa gwamnati dole ne ta dauki matakan gaggawa don hana ficewar kamfanonin ketare.
A yayin da yake magana da daya daga cikin wakilanmu, Daraktan Gudanarwa na Cowry Asset Management Company, Johnson Chukwu, ya bayyana cewa haduwar rikicin kudin waje da rashin daidaito a kimar musayar kudi ya yi tasiri mara kyau ga ra’ayin masu zuba jari na kasashen waje wajen ci gaba da shiga harkokin zuba jari na kamfanoni masu zaman kansu a kasar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA