An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York
Published: 25th, September 2025 GMT
Bugu da kari, mahalarta bikin sun bayyana cewa, bikin ya nuna maimaituwar tarihin MDD na shekaru 80 da suka gabata, tare da yin kira da a karfafa hadin gwiwa tsakanin bangarori daban daban, domin karfafa aniyar al’ummomin kasashen duniya ta kare zaman lafiya, da inganta fahimtar juna.
Haka kuma, Babban rukunin gidan rediyo da talibijin na kasar Sin CMG, ya shirya wani bikin kade-kaden fina-finai masu alaka da zaman lafiya, mai taken “Hadin kai a duniya, Muryar zaman lafiya”, a cibiyar fasaha ta Lincoln da ke birnin New York na kasar Amurka a daren ranar Talata.
Mataimakin sakantaren MDD mai kula da harkokin watsa labarai, Melissa Fleming, ta taya murnar bude bikin ta kafar bidiyo. Haka kuma, shugaban CMG Shen Haixiong, da jakadan Sin a Amurka Xie Feng sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo.
Shen Haixiong ya bayyana cewa, shekaru 80 da suka wuce, bala’o’in yake-yake guda 2 a duniya, sun sa al’ummar duniya yin tunani mai zurfi, kuma MDD ta samu dalilin kafuwa, hakan nan an bude sabon babi na tsarin shugabancin duniya.
A matsayinta na babbar kafar watsa labarai mai sauke nauyi, CMG ta mai da hankali kan ba da labarin ayyukan MDD da kyau, tare da aiwatar da shawarwari 4 na duniya da Shugaba Xi Jinping ya gabatar. Ya ce, “A yau muna amfani da kida don isar da imanin zaman lafiya, muna girmama nasara ta hanyar wakoki, kuma muna hada kan al’umma ta hanyar fasaha. Ta hanyar tattaunawa, muna karfafa fahimtar juna tsakanin al’adu, kuma muna ba da gudummawa a bangaren watsa labarai ga ci gaban tsarin shugabancin duniya tsakanin mabanbantan bangarori.” (Masu Fassara: Maryam Yang, Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon Dake Takawa Makiya Birki
Kwamandan rundunar soja ta “Sayyidush-shuhada” dake Tehran Janar Qurbani Muhammad Wali Zadeh ya bayyana cewa; makamai masu linzami da Iran take da su ne, da kuma jiragen sama marasa matuki suke takawa makiya birki.”
Janar Qurbani Muhammad Wali Zadeh ya kuma ce; Albarkacin sadaukar da jinanai da shahidai su ka yi ne da kuma kwazon kwararrun masana, su ka sa Iran samun wannan karfin da take da shi.
Wali Zadeh wanda ya halarci taron girmama rundunar sa-kai ta Basiji da kudancin birnin Tehran, ya kara da cewa, Iran ta samu matsayin da take da shi ne a wannan lokacin daga jihadin shahidai da tsayin dakar al’ummar Iran, sannan kuma ya kara da cewa; A halin yanzu karfin Iran a fagen makamai masu linzami ya kai kolin da makiya suka kwana da sanin cewa duk wata barazana ta kawo wa jamhuriyar musulunci hari, zai fuskanci martani mai tsanani.
Haka nan kuma ya ce; Al’ummar Iran ba ta taba zama mai tsokana da fara kai hari ba a cikin kowane fada, amma kuma ba ta ja da baya a gaban barazanar makiya.
Janar din sojan na Iran ya yi Ishara da martanin da Iran din ta mayar bayan shahadar Janar Shahid Kassim Sulaimani da ya tabbatar da karfinta na kare kai. Wannan karfin ne yake hana abokan gaba tarbar aradu da ka, su kawo wa Iran din hari.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC November 27, 2025 HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan November 27, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza November 26, 2025 Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa November 26, 2025 Sojoji Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar Guinea Bissau November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci