Gwamnatin Katsina ta kori ma’aikata da malaman makaranta na bogi 3,488
Published: 25th, September 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Katsina ta kori ma’aikata 3,488 daga ƙananan hukumomi 34 da hukumomin ilimi na ƙananan hukumomi (LEA) bayan wani binciken tantance su ya bankado badakala.
Gwamnan jihar, Dikko Radda, wanda ya karɓi rahoton kwamitin a ranar Laraba, ya ce an tantance ma’aikata 50,172, inda aka tabbatar da sahihancin 46,380, yayin da sauran suka bayyana da takardun bogi, takardun daukar aiki na ƙarya, wasu kuma suka ki bayyana a gaban kwamitin.
An gabatar da rahoton a zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar, inda manyan jami’an gwamnati da mambobin kwamitin tantancewa suka halarta.
A cewar rahoton, a karon farko a tarihi, an samar da kundin bayanan dukkan ma’aikatan a intanet, kuma ana sa ran samun rarar Naira miliyan 453.3 a kowane wata idan aka aiwatar da shawarwarin kwamitin.
Kwamitin mai mambobi 10 ya gano takardun haihuwa na bogi, ɗaukar ma’aikata ƙasa da shekarun da doka ta tanada, yin karin matsayi ba bisa ka’ida ba, da kuma bayar da guraben aiki ga wasu maimakon ainihin wadanda aka ɗauka.
Haka kuma, an dawo da Naira miliyan 4.6 daga hannun jami’ai da ke karɓar albashi sau biyu ko kuma suna karɓar albashi yayin da suke hutun aiki.
Shugaban kwamitin, Abdullahi A. Gagare, ya bayyana cewa an bankado Sakataren Ilimi na Zango LEA da ake zargin ya haɗa baki da wasu don saka ma’aikata 24 na ƙarya, yana mai cewa hakan “babban cin amanar aiki ne.”
Gwamna Radda ya ce, “Mun daɗe a cikin tsarin, kuma mun san irin waɗannan abubuwa suna faruwa. Mutane da dama sun yi korafi, har ma sun gargaɗe ni cewa aikin kwamitin zai iya lalata siyasar da nake yi kuma ya janyo min faduwa zaɓe.
“Amma duk da haka ban damu ba, domin halin da Katsina ke ciki yana buƙatar gyara tsarin da yin abin da ya dace.”
Gwamnan ya kuma ce a halin yanzu ƙananan hukumomi sun sami rarar kudi har kusan Naira miliyan 500, wanda zai kai Naira biliyan 5.7 idan aka aiwatar da shawarwarin kwamitin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Korar ma aikata
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
Daga Sani Sulaiman
Gwamnan Jihar Taraba, Dr. Agbu Kefas, ya yi jimami kan rasuwar fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, wanda ya rasu a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamban 2025, yana da shekaru 102.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai bai wa gwamnan shawara na musamman kan Yada Labarai da Hulda da Jama’a, Mista Emmanuel Bello, ya sanyawa hannu.
Gwamnan ya ce rasuwar wannan babban malami babban rashi ne ga kasa, yana mai nuna cewa a wannan lokaci ne ake matuƙar bukatar irin gudummawar da yake bayarwa, duba da kalubalen da kasar ke fusfuskanta.
Ya kara da cewa marigayi Sheikh ya koyar da ilimi da zai ci gaba da jagorantar kasa kan batun zaman lafiya tsakanin addinai.
Haka kuma, Dr. Kefas ya yabawa halayen Sheikh Bauchi, wanda ya bayyana shi a matsayin mutum mai tawali’u, jin kai, da haƙuri.
Saboda haka, Gwamna Agbu Kefas ya yi kira ga jama’a da su yi koyi da jagorancin wannan fitaccen malami.
Ya ce al’ummar kasa za su ci gaba da bin tsarin ladabi da tarbiyyar da marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya koyar.
A wani bangaren, Dr. Kefas ya ja hankalin ‘yan Najeriya da su ci gaba da kasancewa cikin zaman lafiya da juna ba tare da la’akari da addininsu ba.
Ya jaddada muhimmancin jurewa da girmama ra’ayin juna maimakon nacewa a kan namu ra’ayin, tare da tabbatar da aniyarsa ta ci gaba da hidima ga dukkan ‘yan Jihar Taraba bisa adalci ba tare da la’akari da addini ko kabilarsu ba.