Gwamnatin Katsina ta kori ma’aikata da malaman makaranta na bogi 3,488
Published: 25th, September 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Katsina ta kori ma’aikata 3,488 daga ƙananan hukumomi 34 da hukumomin ilimi na ƙananan hukumomi (LEA) bayan wani binciken tantance su ya bankado badakala.
Gwamnan jihar, Dikko Radda, wanda ya karɓi rahoton kwamitin a ranar Laraba, ya ce an tantance ma’aikata 50,172, inda aka tabbatar da sahihancin 46,380, yayin da sauran suka bayyana da takardun bogi, takardun daukar aiki na ƙarya, wasu kuma suka ki bayyana a gaban kwamitin.
An gabatar da rahoton a zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar, inda manyan jami’an gwamnati da mambobin kwamitin tantancewa suka halarta.
A cewar rahoton, a karon farko a tarihi, an samar da kundin bayanan dukkan ma’aikatan a intanet, kuma ana sa ran samun rarar Naira miliyan 453.3 a kowane wata idan aka aiwatar da shawarwarin kwamitin.
Kwamitin mai mambobi 10 ya gano takardun haihuwa na bogi, ɗaukar ma’aikata ƙasa da shekarun da doka ta tanada, yin karin matsayi ba bisa ka’ida ba, da kuma bayar da guraben aiki ga wasu maimakon ainihin wadanda aka ɗauka.
Haka kuma, an dawo da Naira miliyan 4.6 daga hannun jami’ai da ke karɓar albashi sau biyu ko kuma suna karɓar albashi yayin da suke hutun aiki.
Shugaban kwamitin, Abdullahi A. Gagare, ya bayyana cewa an bankado Sakataren Ilimi na Zango LEA da ake zargin ya haɗa baki da wasu don saka ma’aikata 24 na ƙarya, yana mai cewa hakan “babban cin amanar aiki ne.”
Gwamna Radda ya ce, “Mun daɗe a cikin tsarin, kuma mun san irin waɗannan abubuwa suna faruwa. Mutane da dama sun yi korafi, har ma sun gargaɗe ni cewa aikin kwamitin zai iya lalata siyasar da nake yi kuma ya janyo min faduwa zaɓe.
“Amma duk da haka ban damu ba, domin halin da Katsina ke ciki yana buƙatar gyara tsarin da yin abin da ya dace.”
Gwamnan ya kuma ce a halin yanzu ƙananan hukumomi sun sami rarar kudi har kusan Naira miliyan 500, wanda zai kai Naira biliyan 5.7 idan aka aiwatar da shawarwarin kwamitin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Korar ma aikata
এছাড়াও পড়ুন:
Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan yadda shugaba Bola Tinubu ya yi wa wasu mutane afuwa, ciki har da waɗanda suka aikata manyan laifuka.
A cikin saƙon da Atiku ya wallafa a shafinsa na X, ya ce ana yin afuwa ne ga waɗanda aka yi wa rashin adalci ko waɗanda suka nema gafara bayan sun shafe wani lokaci a gidan yari.
Yajin Aikin ASUU: Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a KadunaYa ce a wannan karon an yi wa masu safarar ƙwayoyi, masu garkuwa da mutane, masu kisan kai, da kuma masu cin hanci da rashawa afuwa.
Atiku, ya ce abin mamaki ne yadda gwamnati ke yafewa irin waɗannan mutane, a daidai lokacin da ƙasar ke fama da matsalar tsaro da lalacewar tarbiyya, musamman tsakanin matasa masu shan miyagun ƙwayoyi.
Ya ce bincike ya nuna cewa kashi 29 na waɗanda aka yi wa afuwa suna da alaƙa da hakrar miyagun ƙwayoyi, yayin da Najeriya ke ƙoƙarin wanke sunanta a idon duniya kan yaƙi da miyagun ƙwayoyi.
Atiku, ya ce maimakon wannan afuwa ta zama darasi ga masu laifi, ta zama hanyar durƙusa da ɓangaren shari’a da jami’an tsaro da ke sadaukar da rayukansu wajen kamawa da hukunta masu aikata laifuka.
Ya ƙara da cewa idan gwamnati ta fara yafe wa masu laifi, hakan zai rage ƙimar shugabanci kuma ya ƙarfafa wa masu aikata laifuka su ci gaba da aikata su.
Atiku ya jaddada cewa Najeriya tana buƙatar shugabanci na gari wanda zai tabbatar da adalci a shari’a, ba tare da nuna bambanci ba.