Aminiya:
2025-11-03@20:03:19 GMT

Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump

Published: 3rd, November 2025 GMT

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce ƙasarsa na shirin ɗaukar matakan soja da ka iya haɗawa da hare-haren ƙasa da na sama a Nijeriya.

Trump ya bayyana haka ne yayin da yake tattaunawa da manema labarai, inda yake amsa tambayar yanayin yadda hare-haren za su kasance ta sama ko ta ƙasa.

NAJERIYA A YAU: Ko Kawo Dakarun Amurka Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya? Tsagin Damagum da Anyanwu sun shirya mamaye hedikwatar PDP a yau

A cewarsa, “komai na iya faruwa, abubuwa da dama za su faru.

Ina nufin abubuwa masu yawa,” in ji shi kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya ruwaito.

Shugaban ya ƙara da cewa, “Suna kashe Kiristoci, kuma suna kashe su da yawa. Ba za mu bari hakan ta ci gaba da faruwa ba.”

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta a ranar Asabar, Trump ya bayyana cewa ya umarci Ma’aikatar Tsaron Amurka ta Pentagon da ta tsara yiwuwar kai hari kan Najeriya.

Wannan na zuwa ne kwana guda bayan ya yi gargaɗin cewa Kiristoci na fuskantar kisan kiyashi a ƙasar.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta ce tana kallon wannan batu a matsayin lamarin da za a iya warwarewa ta hanyar diflomasiyya, tana mai cewa ƙasashen biyu abokan hulɗa ne wajen yaƙi da ta’addanci.

Cikin wani saƙo da mai magana da yawun fadar gwamnatin Nijeriya Daniel Bwala ya wallafa ranar Lahadi, ya ce idan shugabannin ƙasashen biyu suka gana, akwai fatan samun mafita mai kyau.

Barazanar Trump

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Truth Social da tsakiyar daren ranar Asabar, Donald Trump ya ce Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya nan take idan har gwamnati ta ci gaba da nuna halin ko in kula kan kisan da ake yi wa mabiya addinin Kirista a kasar.

Hakazalika, Trump ya ce Amurka na iya kutsa wa Nijeriya da ƙarfin soji domin kakkabe ’yan ta’adda masu aikata ta’asa da sunan addinin Islama, sannan ya umurci Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka da ta shirya domin yiwuwar kai wa Nijeriya samame.

Wannan furici na Trump na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatinsa ta saka Najeriya a jerin ƙasashen da ake yi wa Kirista kisan ƙare dangi, zargin da fadar mulki ta Abuja ta musanta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka

Wasu lauyoyi biyu a Najeriya sun gargaɗi Gwamnatin Tarayya da ta yi taka-tsantsan wajen yin hulɗa da ƙasar Amurka, inda suka ce maganganun Amurka a kan Najeriya abun ruɗarwa ne 

Babban lauyan nan, Cuf Okoi Obono-Obla, wanda tsohon mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara ne, ya zargi Amurka da son raba kan ’yan Najeriya da sunan kare Kiristoci.

Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 

Ya ce iƙirarin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya ƙarya ne face nufin tayar da hankali da kawo rikici.

“Najeriya ba ta taɓa zama barazana ga zaman lafiyar duniya ba,” in ji Obono-Obla.

“Idan Amurka, inda ake yawan harbe mutane a coci-coci, ba ta gayyaci sojojin ƙetare su shigo musu ba, to kamata ya yi ta bar Najeriya ta magance nata matsalolin.”

Ya yi gargaɗin cewa duk wani yunƙurin Amurka na yin katsa-landan cikin harkokin Najeriya zai zama take doka da tauye ikon ƙasa.

Shi ma Barista Leonard Anyogo, kuma shugaban ƙungiyar ‘Good Governance Advocacy International’, ya shawarci Najeriya da ta bi hanyoyin diflomasiyya wajen mayar wa Amurka martani ba da faɗa ba.

“Ya kamata mu tattauna, ba mu yi fada ba,” in ji Anyogo.

“Najeriya ta nemi haɗin kai da Amurka a fannin tsaro da diflomasiyya domin kare muradunta.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barazanar kawo hari abin ɗaga hankali ne ga duk ’yan Nijeriya — Peter Obi
  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi