Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Published: 18th, May 2025 GMT
Sojojin Yemen sun kai hari filin jirgin saman Ben Gurion da makami mai linzami guda biyu da kuma jirgin sama mara matuki ciki
Sojojin Yemen sun sanar a yau Lahadi cewa: Sun kai hari kan filin tashi da saukar jiragen sama na Ben Gurion da ke yankin Jaffa da aka mamaye da makamai masu linzami guda biyu da kuma jirgin sama maras matuki ciki.
A cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar ta bayyana cewa: Sojojin Yemen sun kai hari da makami mai linzami kan filin tashi da saukar jiragen sama na Ben Gurion da ke Jaffa da makami mai linzami guda biyu, daya daga cikin makami mai linzami na Falastinu 2 da kuma makami mai linzamin Dhu al-Fiqar.
Sanarwar ta tabbatar da cewa, harin ya samu nasarar cimma burinsa, wanda ya sa miliyoyin ‘yan sahayoniya suka garzaya zuwa maboyar karkashin kasa, tare da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin na kusan sa’a guda.
Majiyar ta kara da cewa: Rundunar sojin sama ta kai wani samame a jiya da safe a kan tashar jirgin saman Ben Gurion da wani jirgin yaki maras matuki da ke Yaffa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Tace Zata Maida Martani Kan Hukumar IAEA
Iran ta bada sanarwan cewa ta sharia matakan da zata dauka kan hukuma IAEA mau kula da makamashin nukliya ta duniya idan ta samar da kudurin yin allawadai ko kuma rashin bada ahadin kai ga hukumar.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’ik Baghae yana fadara haka a jiya Talata . Ya kuma kara da cewa martani da zata mayar tare da hadin kai da hukumar makamashin nukliya ta kasar wato ko Atomic Energy Organization of Iran (AEOI).
Baghae yayi allawadai da rahoton da Daraktan hukumar IAEA Rafael Grossi ya bayar dangane da shirin Nukliyar kasar kafin taron gwamnonin hukumar.
Yace wannan a fili ya nuna cewa hukumar AIEA tana aiki ne don dadadwa makiyan JMI wato Amurka da HKI. Grossi a rahotonsa ya bayyana cewa Iran ta ki ta bayyana ayyukan nukliyan da take yi a wurare uku a cikin kasar. Da kuma yadda ta tache makamancin Uranium har zuwa kashi 60%.
Ya kammala da cewa Iran ta dade tana shakkan ayyukan shugaban hukumar Makamashin nukliya ta IAEA, amma a cikin wasikun sirri da suka samu ta hanyar leken asiri sun tabbatar da abinda muke shakka.
Mohammad Eslamu daractan hukumar makamashin Nukliya ta kasar ya yi tir da rahoron grossi wanda a fili yana taimakawa maikan JMI a dai dai lokacinda yakamata a zama dan ba ruwammu ya daina shiga harkokin siyasa. Banda haka rahoton nasa bai da kima ga kwarraru wadanda suka san ayyukan makamashin nukliya.