Sojojin Yemen sun kai hari filin jirgin saman Ben Gurion da makami mai linzami guda biyu da kuma jirgin sama mara matuki ciki

Sojojin Yemen sun sanar a yau Lahadi cewa: Sun kai hari kan filin tashi da saukar jiragen sama na Ben Gurion da ke yankin Jaffa da aka mamaye da makamai masu linzami guda biyu da kuma jirgin sama maras matuki ciki.

A cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar ta bayyana cewa: Sojojin Yemen sun kai hari da makami mai linzami kan filin tashi da saukar jiragen sama na Ben Gurion da ke Jaffa da makami mai linzami guda biyu, daya daga cikin makami mai linzami na Falastinu 2 da kuma makami mai linzamin Dhu al-Fiqar.

Sanarwar ta tabbatar da cewa, harin ya samu nasarar cimma burinsa, wanda ya sa miliyoyin ‘yan sahayoniya suka garzaya zuwa maboyar karkashin kasa, tare da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin na kusan sa’a guda.

Majiyar ta kara da cewa: Rundunar sojin sama ta kai wani samame a jiya da safe a kan tashar jirgin saman Ben Gurion da wani jirgin yaki maras matuki da ke Yaffa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa October 10, 2025 Daga Birnin Sin Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka October 10, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata   October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni
  • Iran Ta Gayyaci Mukaddashin Jakadan Kasar Oman Zuwa Ma’aikatar Harkokin Wajenta
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta
  • Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk
  • Kasar Indunusiya Ta Hana Tawagar wasan Jiminastik din Isra’ila Visar Shiga Kasarta
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Pakistan Ta Kai Hari Kan Kasar Afganistan, Inda Ake Rade-Radin Kashe Shugaban Taliban Na Kasarta
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Sojojin Ruwan Sin Za Su Gudanar Da Aikin Sintiri A Zirin Tekun Aden Da Yankin Tekun Somaliya
  • Sa’o’ii Da Fara Janyewar Sojojin HKI A Gaza An Fara Gano Gawakin Falasdinwa