HausaTv:
2025-05-18@09:46:18 GMT

An yi zanga-zanga zagayowar ranar ‘’Nakba’’ a sassan duniya da dama

Published: 18th, May 2025 GMT

An gudanar da zanga-zangar nuna goyon baya ga al’ummar Falasdinu a sassa daban-daban na duniya, a yayin zagayowar cika shekaru 77 da ranar ‘’Nakba’’ cewa da masifa.

A Faransa da Ingila duk an gudanar da wannan zanga zanga a wasu sassan kasar.

A cikin jerin gwanon, an daga allunan da ke dauke da sakonni irin su “Falasdinu za ta rayu!” » ko “Dakatar da kisan kiyashi a Gaza”.

“Nakba ba wani lamari ne da ya faru a baya ba, yana ci gaba da faruwa ta hanyar korar jama’a, da amfani da bama-bamai,” kan al’ummar Gaza.

Masu zanga-zangar sun yi Allah wadai da tabarbarewar al’amuran jin kai a zirin Gaza tun bayan barkewar yakin kisan kiyashi da Isra’ila ta kaddamar a watan Oktoban 2023 bayan harin ba-zata da Hamas ta kai.

Masu zanga zangar dake dauke da tutocin Falasdinu a Paris, sun zargi hukumomin Faransa, da yin hadin gwiwa da Isra’ila ta hanyar yin gum da bakinsu.”

A Zirin Gaza tun daga ranar 18 ga watan Maris din 2025, lokacin da gwamnatin Sahayoniya ta ci gaba da kai hare-hare, tare da karya yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Hamas da ta fara aiki a ranar 19 ga watan Janairu, an kashe Falasdinawa sama da 3,000, lamarin da ya kawo adadin wadanda suka mutu a Gaza tun farkon yakin zuwa akalla mutane 53,272, galibi mata da kananan yara, sannan Fiye da mutane 120,673 kuma sun jikkata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce Amurka Tana Da Hannu Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Gaza

Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa: Amurka tana da hannu dumu-dumu a muggan ayyukan da gwamnatin ‘yan shayoniyya suka aikata nakisan kare dangi a Gaza

Jakada kuma wakilin dindindin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya Amir Sa’ed Irawani ya yi nuni da ire-iren laifuffukan da gwamnatin ‘yan sahayoniyya suke ci gaba da aikatawa kan al’ummar Falastinu, yana mai bayyana wadannan laifuka a matsayin wani misali karara na kisan kiyashi yana kuma daukar Amurka a matsayin babbar kawa a aikata wadannan muggan laifuka.

A yayin zama na musamman a Majalisar Dinkin Duniya a yammacin jiya Alhamis kan batun boren Falasdinawa “Ankaba” na musamman ya bayyana cewa: Gwamnatin yahudawan sahayoniyya tana so da cikakken goyon baya da taimakon Amurka ta hanyar kaddamar da harte-haren wuce gona da iri da gangan ta rusa asibitoci, makarantu, kashe mata da yara, kaiwatar da kisan gilla kan ma’aikatan Majalisar Dinkin Duniya da ‘yan jarida da sauransu, lamarin da a halin yanzu ya yi sanadin shahadar mutane kusan 60,000 da jikkata wasu da kuma bacewar wasu da dama.

Babban jami’in diflomasiyyar Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya kara da cewa: Munanan laifukan da gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta aikata, ba za a iya musantawa ba, kuma kungiyoyin duniya, kotun duniya da sauran hukumomin shari’a na da masaniya kan irin girman wadannan munanan ayyukan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Ce An Fara Tattaunawa Tare Da HKI Kan Tsakana Wuta A Doha A Yau Asabar
  • Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada
  • Max Air Zai Yi Jigilar Alhazan Jihar Jigawa A Ranakun 20 Da 21 Ga Watan Mayu
  • Dubban Falasdinawa Sun Fito Kan Titunan NewYork Don Tunawa Da Ranar Musiba ko Nakba
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa Akalla 143 A Ranar Tunawa Da Musibar Nakba
  • Iran Tace Ranar Nakba Farawa Ce Na Musibu Ba Karshensu Ba
  • Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Ya Ce Amurka Tana Da Hannu Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Gaza
  • Kungiyar Hamas Ta Shirya Zanga-Zangar Goyon Bayan Halaccin Yunkurin ‘Yantar Da Kasarsu Daga Mamayar Yahudawa
  • Qalibaf : Dole ne Iran da Aljeriya su hada kai don saukaka kai kayan agaji zuwa Gaza