Aminiya:
2025-07-02@17:07:24 GMT

Crystal Palace ta lashe kofin FA na farko a tarihinta

Published: 17th, May 2025 GMT

Crystal Palace ta doke Manchester City da ci ɗaya mai ban haushi a filin wasa na Wembley a ranar Asabar, inda ta lashe Kofin FA karo na farko a tarihinta.

Eberechi Eze ne, ya zura ƙwallo ɗaya tilo tun da aka fara wasan, yayin da mai tsaron ragar Crystal Palace, Dean Henderson ya taka rawar gani a wasan wajen hana Man City zura ƙwallo.

Ban sauya sheƙa ba, makircin siyasa da ƙarya ake min — Kwankwaso  Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya

Man City ta rasa damar yin kunnen doki a wasan bayan Omar Marmoush ya kasa cin bugun daga kai sai mai tsaron raga.

Henderson, ya tsallake rijiya da baya, bayan duba VAR kan yiwuwar ko hannunsa ya taɓa ƙwallon a wajen yadi na 18.

Wannan nasara ce ta farko da Palace ta taɓa samu a gasar manyan kofuna cikin shekaru 120.

Man City kuwa, wannan na nuna cewar kakar wasanninta ta bana an yi uwa kwance ɗa kwance, wato ba ta lashe kowane kofi ba, hakan na iya ƙara wa kocinta, Pep Guardiola matsin lamba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Crystal Palace Ƙwallo Wasan Ƙarshe

এছাড়াও পড়ুন:

APC ta sa ranar taron Majalisar Zartarwa bayan murabus ɗin Ganduje

Jam’iyyar APC mai mulki a Nijeriya ta tsayar da 24 ga watan Yulin bana a matsayin ranar da za ta gudanar da taronta na Majalisar Zartarwa.

Mataimakin Sakataren jam’iyyar, Barista Fetus Fuanter ne ya tabbatar wa manema labarai hakan a yau Litinin a Abuja.

Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe Jami’an tsaro sun hana taron kwamitin amintattun PDP

Fuanter ya ce kusoshin jam’iyyar za su gana kafin gudanar da taron Majalisar Zartarwar.

Taron da za a gudanar shi ne na biyu ta fuskar girma a cikin jerin tarukan da jam’iyya ke zaman yanke shawara da daukar wasu muhimman matakai bayan babban taronta na kasa.

Wannan dai na zuwa ne yayin da ake ci gaba cece-kuce tun bayan murabus ɗin shugaban jam’iyyar na ƙasa ya yi a makon jiya.

A makon da ya gabata ne shugaban jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar, Abdullahi Ganduje, ya ajiye mulki a wani abu da masana ke cewa na da alaƙa da lisaafin da manyan ’yan siyasar ke yi gabanin Zaɓen 2027.

APC ta ce tuni Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya umarci Ali Bukar Dalori ya maye gurbin Ganduje a matsayin shugaba na riƙo kafin kwamatin zaɓaɓɓu su gana game da batun.

Jami’in yaɗa labarai na APC, Bala Ibrahim, ya bayyana cewa babban dalilin da Ganduje ya bayar game da murabus ɗin nasa shi ne batun ƙoshin lafiyarsa.

Sai dai wata majiya daga fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa Ganduje ya ajiye muƙamin ne bayan da fadar shugaban ta umarce shi da yin hakan.

Da ma tun lokacin aka bai wa Ganduje shugabancin jam’iyyar wasu ‘yan jam’iyyar, musamman daga yankin Arewa maso Gabas, suka riƙa gunaguni cewa su ya kamata a bai wa.

Zuwa yanzu babu tabbas game da wanda fadar shugaban ke son ya karɓi shugabancin jam’iyyar.

Daga cikin waɗanda ake raɗe-raɗin za su maye gurbin Ganduje akwai tsohon Gwamnan Nasarawa, Umar Tanko Al-Makura da Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen VC Na Jami’ar Bayero Ta Kano 
  • Sai bayan Magariba za a yi wa Dantata jana’iza a Madina
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu
  • Isra’ila na neman ƙulla hulɗa da Siriya da Lebanon
  • Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
  • CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata
  • Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
  • APC ta sa ranar taron Majalisar Zartarwa bayan murabus ɗin Ganduje
  • Yau za a yi Jana’izar Aminu Dantata a Madina
  • Tarihi da tasirin rayuwar Alhaji Aminu Alhassan Dantata