Aminiya:
2025-05-17@21:41:56 GMT

Crystal Palace ta lashe kofin FA na farko a tarihinta

Published: 17th, May 2025 GMT

Crystal Palace ta doke Manchester City da ci ɗaya mai ban haushi a filin wasa na Wembley a ranar Asabar, inda ta lashe Kofin FA karo na farko a tarihinta.

Eberechi Eze ne, ya zura ƙwallo ɗaya tilo tun da aka fara wasan, yayin da mai tsaron ragar Crystal Palace, Dean Henderson ya taka rawar gani a wasan wajen hana Man City zura ƙwallo.

Ban sauya sheƙa ba, makircin siyasa da ƙarya ake min — Kwankwaso  Hajj: Ranar Lahadi za a fara jigilar maniyyatan Katsina zuwa Saudiyya

Man City ta rasa damar yin kunnen doki a wasan bayan Omar Marmoush ya kasa cin bugun daga kai sai mai tsaron raga.

Henderson, ya tsallake rijiya da baya, bayan duba VAR kan yiwuwar ko hannunsa ya taɓa ƙwallon a wajen yadi na 18.

Wannan nasara ce ta farko da Palace ta taɓa samu a gasar manyan kofuna cikin shekaru 120.

Man City kuwa, wannan na nuna cewar kakar wasanninta ta bana an yi uwa kwance ɗa kwance, wato ba ta lashe kowane kofi ba, hakan na iya ƙara wa kocinta, Pep Guardiola matsin lamba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Crystal Palace Ƙwallo Wasan Ƙarshe

এছাড়াও পড়ুন:

Rootswatch Ta Karrama Builder Muhammad Uba Da Lambar Yabo Ta Kasa

An karrama Injiniya Dr. Mohammed Uba da lambar yabo ta kasa ta Rootswatch ta shekarar 2025, a matsayin girmamawa bisa gagarumin gudummawar da ya bayar wajen ci gaban al’umma, aiwatar da muhimman ayyukan raya kasa, da kuma kyakkyawan jagoranci.

An mika wannan lambar yabo ne a yau a Cibiyar Karramawa ta Kasa da Kasa da ke Abuja.

An karrama Dr. Uba tare da wasu shugabannin kananan hukumomi guda uku daga Jihar Jigawa da suka hada da Abdullahi Na Layi, Jarma na Garki, da Malam Madori, saboda hadin gwiwarsu wajen bunkasa ci gaban al’umma tun daga yankunan karkara.

Taron ya jawo hankalin manyan baki daga sassa daban-daban na ƙasar, kuma ya kasance wata hanya ta ƙarfafa gwiwar shugabannin kananan hukumomi wajen ƙara himma a ayyukan da suke yi.

A jawabinsa na godiya, Dr. Uba ya gode wa al’ummar Birnin Kudu bisa goyon bayan da suke ba shi a koda yaushe, tare da alkawarin ci gaba da sadaukarwa wajen hidima ga al’umma.

Ya kuma bayyana godiyarsa ga Gwamna Umar Namadi saboda samar da yanayi mai kyau da ke bai wa kananan hukumomi damar sauya rayuwar al’umma ta hanya mai ma’ana.

Lambar yabon ta sake tabbatar da irin karbuwa da shugabanci nagari ke samu a matakin karkara, tare da haskaka ci gaban da Jihar Jigawa ke samu a ƙarƙashin wannan gwamnati.

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0
  • Shuwagabanin Larabawa Sun Yi Alkawalin Sake Gina Gaza, Suna Kuma Kokarin Tsagaita Wuta Da Farko
  • Iran: Cikakken Goyon Bayan Amurka Ga ‘Yan Sahayoniya Ne Yake Sa Su Tafka Laifuka
  • Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka
  • NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?
  • Qalibaf : Dole ne Iran da Aljeriya su hada kai don saukaka kai kayan agaji zuwa Gaza
  • Rootswatch Ta Karrama Builder Muhammad Uba Da Lambar Yabo Ta Kasa
  • Yoro Da De Light Da Heaven Ba Su Yi Atisaye A Man United Ba
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Da Jirgin Alhazan Kano Na Farko