Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista
Published: 16th, May 2025 GMT
“Wannan ya ba wasu jihohi fiye da goma sha daya ‘yancin kai, tare da karin wadanda ake sa ran za su biyo baya. Wadannan jihohin yanzu suna iya shiga cikin masana’antar wutar lantarki, daga samarwa har zuwa isarwa, rarraba, har ma da samar da mitoci.”
“Na biyu, dole ne mu magance rashin ingancin ababen more rayuwa, wanda ya taru a cikin shekaru 60 da suka wuce saboda rashin kula da rashin isasshen zuba jari don farfado da tsarin zamanantar da wutar lantarki.
Ministan ya kuma jaddada bukatar cike gibin mita na sama da kashi 50 bisa dari, yana mai cewa shirin shugaban kasa yana nufin cimma wannan ta hanyar girka mita miliyan 18 a cikin shekaru biyar masu zuwa.
Ya ce an kaddamar da wutar lantarki ta tashar Solar PV mai karfin 600kW da 3MW a makarantar horar da sojojin Nijeriya domin bai wa gwamnatin tarayya kwarin gwiwa wajen magance karancin wutar lantarki.
Daraktan gudanarwa na Hukumar Wutar Lantarki ta Karkara (REA), Abba Abubakar Aliyu, ya bayyana kaddamar da aikin hasken rana na 2.5MW a matsayin wata mafita ga Nijeriya wajen samun wutar lantarki ga makarantun ilimi.
Ya kara da cewa hukumar ba kawai tana kaddamar fara wani aiki ba ne, tana kuma lura da tasirin zamantakewa, bincike, da ci gaban mai dorewa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Lantarki wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
‘Zan iya shiga mummunan yanayi idan Dangote bai aure ni ba’
Wata ’yar siyasa a jihar Bauchi mai suna Aishatu Haruna, ta ce ta shafe shekaru shida tana dakon soyayyar attajirin nan na Afirka, Alhaji Aliko Dangote a ranta, inda ta ce za ta iya shiga mummunan hali idan bai aure ta ba.
Ta ce sau uku tana yin mafarkin ta aure shi, kuma ba ta jin za ta iya auren wani ba shi ba a duniya.
A cikin wata tattaunawarta da gidan rediyon Albarka da ke jihar Bauchi, Aishatu, wacce aka fi sani da Gimbiyar Mawakan Bauchi, ta kuma ce sau uku tana zuwa kamfanin attajijin na Obajana, ko za ta hadu da shi a can.
Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura Lafiyar Tinubu kalau – SoludoAishatu wacce a 2019 ta yi takarar neman zama Majalisar Jiha dai ta wallafa hotonta ne dauke da katin gayyatar daurin aurenta da attajirin a shafukan sada zumunta, inda ta ce tana ganin ta wannan hanyar ce sakonta zai isa gare shi.
A cewarta, “Ita soyayya a zuci take, kuma ni na gamsu shi nake so, saboda yadda yake amfani da dukiyar da Allah ya ba shi wajen hidimta wa al’umma ba iya Najeriya ba, har ma da Afirka.
“Kusan shekara shida ke nan da farawar abin. Akwai lokacin ma da na yi tattaki na tafi har kamfaninsa na siminta da ke Obajana a jihar Kogi da nufin na gan shi har sau uku, amma bai yiwu ba.
“Dalilin da ya sa na buga katin shi ne saboda na san nan ce hanya mafi sauri da zai san da ni, kuma na san babu abin da ya gagari Allah,” in ji ta.
Sai dai ta tsaya kai da fata cewa ba don dukiyarsa take son shi ba, kawai ji ta yi shi kadai ne ya kwanta mata a ransa.
“Babu wanda aka haifa da dukiya, kuma ba don ita nake son shi ba, don haka ba maganar kwarya ta bi karya don baa bin da ya gagari Allah. Ni kawai yana burge ni ne,” in ji ta.
Ta ce ta gaji da dakon soyayyar a zuciyarta, shi ya sa yanzu ta fito da ita a shafukan sada zumuntar domin kada ta shiga wani halin.