Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista
Published: 16th, May 2025 GMT
“Wannan ya ba wasu jihohi fiye da goma sha daya ‘yancin kai, tare da karin wadanda ake sa ran za su biyo baya. Wadannan jihohin yanzu suna iya shiga cikin masana’antar wutar lantarki, daga samarwa har zuwa isarwa, rarraba, har ma da samar da mitoci.”
“Na biyu, dole ne mu magance rashin ingancin ababen more rayuwa, wanda ya taru a cikin shekaru 60 da suka wuce saboda rashin kula da rashin isasshen zuba jari don farfado da tsarin zamanantar da wutar lantarki.
Ministan ya kuma jaddada bukatar cike gibin mita na sama da kashi 50 bisa dari, yana mai cewa shirin shugaban kasa yana nufin cimma wannan ta hanyar girka mita miliyan 18 a cikin shekaru biyar masu zuwa.
Ya ce an kaddamar da wutar lantarki ta tashar Solar PV mai karfin 600kW da 3MW a makarantar horar da sojojin Nijeriya domin bai wa gwamnatin tarayya kwarin gwiwa wajen magance karancin wutar lantarki.
Daraktan gudanarwa na Hukumar Wutar Lantarki ta Karkara (REA), Abba Abubakar Aliyu, ya bayyana kaddamar da aikin hasken rana na 2.5MW a matsayin wata mafita ga Nijeriya wajen samun wutar lantarki ga makarantun ilimi.
Ya kara da cewa hukumar ba kawai tana kaddamar fara wani aiki ba ne, tana kuma lura da tasirin zamantakewa, bincike, da ci gaban mai dorewa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Lantarki wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Dole Ne Kansiloli Su Shiga Cikin Dukkan Ayyukan Kananan Hukumomin Su – Gwamna Yusuf
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umurci shugabannin kananan hukumomin jihar 44 da su tabbatar da cewa Kansilolinsu sun shiga dukkan ayyukan da aka gudanar a kananan hukumominsu .
Gwamnan ya bayyana haka ne a wata ganawa da ya yi da kansilolin kananan hukumomi 484 daga kananan hukumomi 44 na jihar.
Taron wanda ya gudana a dakin taro na Coronation dake gidan gwamnati, da nufin karfafa alaka tsakanin gwamnatin jihar da majalisun kananan hukumomi.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada cewa gwamnatin sa tana da hankali kuma ba ta da almundahana, kuma ba za a amince da duk wani nau’i na almundahana ba.
Ya kuma bukaci kansilolin da su yi aiki tukuru don ganin sun rike amanar da aka ba su.
Gwamnan ya shawarce su da su yi aiki tare da shugabannin su don inganta ilimi, kiwon lafiya, noma, da kuma ci gaban bil’adama.
Gwamna Yusuf ya umurci kansilolin da su fito da ayyukan da za su amfanar da unguwanninsu, wadanda za a aiwatar da su ne domin amfanin kowa da kowa.
Kwamishinan ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu Muhammad Tajuddeen ya yabawa kokarin kansilolin kananan hukumomin wajen gudanar da harkokin kananan hukumominsu.
Ya bukace su da su ci gaba da marawa manufofin gwamnati baya tare da tabbatar da sun sanar da masu zabe wadannan manufofin.
Shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Ismail Falgore, ya shawarci shugabannin kananan hukumomin da su yi aiki tare da shugabanninsu domin cimma manufofinsu.
Ya kuma yi kira ga gwamnan da ya duba albashi da alawus-alawus na kansilolin kananan hukumomin domin kara musu kwarin gwiwa.
Shugabar Kungiyar Kananan Hukumomin Najeriya (ALGON) reshen Jihar Kano, Hajiya Saadatu Yusha’u, ta yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na taba rayuwar ‘yan Kano ba tare da la’akari da matsayinsa ba.
Shugaban kungiyar kansilan Arewa maso Yamma, Bashir Shehu Achika, ya yaba da kokarin gwamnati mai ci na samar da ababen more rayuwa ga talakawa.
Ya yi nuni da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna jajircewarsa na tallafawa kananan hukumomi ta hanyar ware kudade don gudanar da ayyuka don jin dadin jama’a.
Achika ya roki gwamnatin jihar da ta shirya wani taron karawa juna sani domin bunkasa kwarjinin kansilolin kananan hukumomi domin gudanar da ayyuka masu inganci.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO