Sojojin Yemen Suna Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Babban Filin Jirgin Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Published: 16th, May 2025 GMT
Rundunar sojin Yemen sun kai hari kan filin jirgin saman Ben Gurion da makami mai linzami
Rundunar sojin Yemen ta sanar da kaddamar da farmakin soji kan babban filin tashin jiragen saman Ben Gurion da ke yankin Jaffa da aka mamaye, domin jaddada goyon baya ga al’ummar Falastinu da ake zalunta da kuma yin nuna kiyayya ga kisan kiyashin da makiya ‘yan sahayoniyya suke yi wa ‘yan uwansu a Zirin Gaza.
Kakakin rundunar sojin Yemen Birgediya Janar Yahya Sari’e ya bayyana cewa: Don goyon bayan al’ummar Falastinu da ake zalunta da ‘yan gwagwarmaya da kuma nuna rashin amincewa da kisan kiyashin da makiya ‘yan sahayoniyya suke yi kan ‘yan uwansu a yankin Zirin Gaza, sojojin Yemen suna ci gaba da kai hare-hare da makamai masu linzami kan babban filin jirgin sama na Lod, wanda haramtacciyar kasar Isr’ila ke kira da filin jirgin saman Ben Gurion, a yankin Jaffa da suka mamaye.
Janar Yahya Sari’e ya kara da cewa: Suna kai hare-haren da makamai masu linzami masu linzami, domin tarwatsa yahudawan sahayoniyya ‘yan kaka gida.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ
Hedikwatar Tsaro ta Ƙasa (DHQ), ta ce rahotannin da ake yaɗawa cewar ƙasurgumin ɗan bindiga Bello Turji, ya miƙa wuya ba gaskiya ba ne.
Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Tsaro, Manjo Janar Markus Kangye ne, ya sanar da hakan ga manema labarai a Abuja a ranar Alhamis yayin bayani kan ayyukan sojoji.
Rashin Lantarki: Babu wanda za mu zaɓa a 2027 — Jama’ar Talasse Ba a ba mu dala 100,000 da gwamnati ta mana alƙawari ba — Super FalconsYa ce: “Turji bai miƙa wuya ba. Har yanzu muna neman sa.”
Turji na daga cikin manyan ’yan bindigar da ake nema ruwa a jallo a Najeriya.
Turji ya jagoranci kai wa al’umma hare-hare a Jihohin Zamfara da Sakkwato, inda suka kashe mutane da dama tare da yin garkuwa da wasu.
A kwanakin baya, an samu rahotanni cewa Turji, ya ajiye makamai kuma ya saki mut 32 da ya sace, bayan zaman sulhu da malaman addinin Musulunci suka jagoranta a Jihar Zamfara.
Amma sojojin sun bayyana cewa wannan rahotanni ba gaskiya ba ne.