NUJ Ta Kafa Kwamitin Ladabtarwa A Jigawa
Published: 16th, May 2025 GMT
Kungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Jigawa ta ce ta dauki mataki mai muhimmanci wajen tabbatar da kiyaye ka’idojin aikin jarida ta hanyar kafa Kwamitin Ladabtarwa da kuma Kwamitin Ilimi da Horaswa.
A cikin wata sanarwa da Sakatariyar kungiyar, Kwamared Aisha Abba Ahmed ta fitar, ta bayyana cewa Kwamared Sabo Abdullahi Guri ne zai jagoranci Kwamitin Ladabtarwar tare da Kwamared Mati Ali, da Dr.
Sanarwar ta bayyana cewa an dora wa kwamitin alhakin tabbatar da bin ka’idojin aikin jarida, warware matsalolin rashin ladabi ko sabawa doka cikin aikin, da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana a aikin jarida a jihar Jigawa.
Haka kuma kungiyar ta sanar da kafa kwamitin ilimi da horaswa mai mambobi 7, wanda Kwamared Sani Labaran Salisu zai jagoranta.
Mambobin kwamitin sun hada da Garba Yakubu, Ado Lurwan, Aliyu Dangida, Mustafa Namadi da Balarabe Sani, yayin da Shuaibu Aliyu zai kasance Sakataren kwamitin.
Kwamared Aisha Abba Ahmed ta bayyana cewa an dora wa wannan kwamiti alhakin karfafa gwanintar ‘yan jarida ta hanyar horaswa, taron bita da shirye-shiryen ci gaban aikin su a kai a kai.
Shugaban kungiyar ta NUJ reshen Jigawa, Kwamared Ismail Ibrahim Dutse, ya jaddada cewa kafa wadannan kwamitoci ya nuna kudurin kungiyar wajen karfafa kwararru, gaskiya da inganci a cikin aikin jarida.
Majalisar ta kuma bukaci dukkan mambobi da su ba da cikakken hadin kai ga kwamitocin domin cimma burinsu na ci gaban kungiyar da aikin jarida baki daya.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa aikin jarida
এছাড়াও পড়ুন:
Leroy Sane ya koma Galatasaray
Kungiyar kwallon kafa ta Galatasaray a wannan Alhamis din ta sanar da daukar dan wasan Jamus, Leroy Sane daga Bayern Munich.
Kungiyar ta Turkiyya ta dauki dan wasan ne kyauta bayan kwantaraginsa ya kare a Munich.
Mayar da Nijeriya tsarin jam’iyya ɗaya ba ya cikin manufofinmu — Tinubu Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – ManeSane mai shekaru 29 ya rattaba hannu kan kwantaragin shekaru uku inda zai rika daukar albashin Yuro miliyan 9 — kwantankwacin Dala miliyan 10.4 — duk shekara kamar yadda kulob din bayyana.
Sane ya buga wa kasarsa ta Jamus wasanni 70, inda kuma ya lashe kofunan Bundesliga guda hudu a Bayern Munich tun bayan raba gari da Manchester City, inda ya dauki Firimiyar Ingila guda biyu.A kakar bana Sane ya jefa kwallaye 13 a duk gasannin da ya haska, inda ya taimaka wa Bayern lashe gasar Bundesliga bayan ta subuce daga hannunta a kakar bara.
AFP