NUJ Ta Kafa Kwamitin Ladabtarwa A Jigawa
Published: 16th, May 2025 GMT
Kungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Jigawa ta ce ta dauki mataki mai muhimmanci wajen tabbatar da kiyaye ka’idojin aikin jarida ta hanyar kafa Kwamitin Ladabtarwa da kuma Kwamitin Ilimi da Horaswa.
A cikin wata sanarwa da Sakatariyar kungiyar, Kwamared Aisha Abba Ahmed ta fitar, ta bayyana cewa Kwamared Sabo Abdullahi Guri ne zai jagoranci Kwamitin Ladabtarwar tare da Kwamared Mati Ali, da Dr.
Sanarwar ta bayyana cewa an dora wa kwamitin alhakin tabbatar da bin ka’idojin aikin jarida, warware matsalolin rashin ladabi ko sabawa doka cikin aikin, da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana a aikin jarida a jihar Jigawa.
Haka kuma kungiyar ta sanar da kafa kwamitin ilimi da horaswa mai mambobi 7, wanda Kwamared Sani Labaran Salisu zai jagoranta.
Mambobin kwamitin sun hada da Garba Yakubu, Ado Lurwan, Aliyu Dangida, Mustafa Namadi da Balarabe Sani, yayin da Shuaibu Aliyu zai kasance Sakataren kwamitin.
Kwamared Aisha Abba Ahmed ta bayyana cewa an dora wa wannan kwamiti alhakin karfafa gwanintar ‘yan jarida ta hanyar horaswa, taron bita da shirye-shiryen ci gaban aikin su a kai a kai.
Shugaban kungiyar ta NUJ reshen Jigawa, Kwamared Ismail Ibrahim Dutse, ya jaddada cewa kafa wadannan kwamitoci ya nuna kudurin kungiyar wajen karfafa kwararru, gaskiya da inganci a cikin aikin jarida.
Majalisar ta kuma bukaci dukkan mambobi da su ba da cikakken hadin kai ga kwamitocin domin cimma burinsu na ci gaban kungiyar da aikin jarida baki daya.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa aikin jarida
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iraki Ya Bukaci Zaman Tattaunawa Tsakanin Kungiyar Larabawan Yankin Tekun Gulf Da Iraki Da Kuma Iran
Ministan harkokin wajen kasar Iraki ya ba da shawarar gudanar da taron kasashen Larabawan yankin tekun Pasha da Iraki da kuma Iran
Ministan harkokin wajen kasar Iraki Fuad Hussein ya gabatar da shawarar gudanar da taron hadin gwiwa tsakanin kasashen Iraki, Iran, da kuma kasashen larabawan yankin Gulf, a tsarin na 6+2, a gefen taron majalisar dinkin duniya.
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar Iraki ta fitar ta bayyana cewa: Mataimakin fira ministan kasar ta Iraki, kuma ministan harkokin wajen kasar Fuad Hussein ya gana da Ali Larijani, sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran.
Sanarwar ta bayyana cewa, a yayin ganawar, an tattauna dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da aikin layin dogo da zai hada Shalamcheh da Basra, da kuma kalubalen da ke gaban kammala shi, da suka hada da kawar da ma’adanai da sauran cikas, an kuma amince da cewa, hukumomin da abin ya shafa daga bangarorin biyu, za su bi diddigin lamarin, don nemo hanyoyin da suka dace.
Bayanin ya ci gaba da cewa: An kuma tattauna batun tsawaita layin dogon daga yankin Khosravi da ke bangaren Iran zuwa Khanaqin da Bagadaza, kuma an jaddada muhimmancin fara bincike kan aikin, bisa la’akari da tasirin da yake da shi wajen karfafa dangantakar tattalin arziki da karfafa harkokin yawon bude ido na addini, da kuma yiwuwar alakanta wannan layin da aikin hanyar raya kasa a nan gaba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Italiya Ta Janye Jirgin Ruwanta Daga Taken Bahar Maliya Saboda Barazanar ‘Yan Gwagwarmayar Yemen August 12, 2025 Majalisar Dinkin Duniya Ta Sanar Da Mutuwan Mutane 60 Saboda Yunwa A El-Fasher Na Sudan August 12, 2025 Iran da Iraki sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro August 12, 2025 Masar ta yi gargadin daukar tsauraran matakai domin kare muradunta August 12, 2025 Iran ta yi Allah wadai da kisan kiyashin da Isra’ila ta yi wa ‘yan jarida a Gaza August 12, 2025 Gaza: Yunwa ta kashe Falastinawa 5 a cikin kasa da Sa’o’i 24 da suka gabata August 12, 2025 Ministan tsaron Italiya ya caccaki gwamnatin Netanyahu kan batun Gaza August 12, 2025 Araghchi: Mataimakin Shugaban IAEA Zai Ziyarci Tehan َA Wannan Talata August 11, 2025 Iran: Lebanon Tana Da ‘Yancin Kare Kanta Da Makamanta August 11, 2025 Mali: An Kama Sojoji Fiye da 40 Bisa Zargin Yunkurin Juyin Mulki August 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci