Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-15@23:46:21 GMT

NUJ Ta Kafa Kwamitin Ladabtarwa A Jigawa

Published: 16th, May 2025 GMT

NUJ Ta Kafa Kwamitin Ladabtarwa A Jigawa

Kungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Jigawa ta ce ta dauki mataki mai muhimmanci wajen tabbatar da kiyaye ka’idojin aikin jarida ta hanyar kafa Kwamitin Ladabtarwa da kuma Kwamitin Ilimi da Horaswa.

A cikin wata sanarwa da Sakatariyar kungiyar, Kwamared Aisha Abba Ahmed ta fitar, ta bayyana cewa Kwamared Sabo Abdullahi Guri ne zai jagoranci Kwamitin Ladabtarwar tare da Kwamared Mati Ali, da Dr.

Musa Idris Barnawa da Yusuf Sulaiman a matsayin mambobi, yayin da Muhammad Askira Musa zai kasance Sakataren kwamitin.

Sanarwar ta bayyana cewa an dora wa kwamitin alhakin tabbatar da bin ka’idojin aikin jarida, warware matsalolin rashin ladabi ko sabawa doka cikin aikin, da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana a aikin jarida a jihar Jigawa.

Haka kuma kungiyar ta sanar da kafa kwamitin ilimi da horaswa mai mambobi 7, wanda Kwamared Sani Labaran Salisu zai jagoranta.

Mambobin kwamitin sun hada da Garba Yakubu, Ado Lurwan, Aliyu Dangida, Mustafa Namadi da Balarabe Sani, yayin da Shuaibu Aliyu zai kasance Sakataren kwamitin.

Kwamared Aisha Abba Ahmed ta bayyana cewa an dora wa wannan kwamiti alhakin karfafa gwanintar ‘yan jarida ta hanyar horaswa, taron bita da shirye-shiryen ci gaban aikin su a kai a kai.

Shugaban kungiyar ta NUJ reshen Jigawa, Kwamared Ismail Ibrahim Dutse, ya jaddada cewa kafa wadannan kwamitoci ya nuna kudurin kungiyar wajen karfafa kwararru, gaskiya da inganci a cikin aikin jarida.

Majalisar ta kuma bukaci dukkan mambobi da su ba da cikakken hadin kai ga kwamitocin domin cimma burinsu na ci gaban kungiyar da aikin jarida baki daya.

 

Usman Muhammad Zaria 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa aikin jarida

এছাড়াও পড়ুন:

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe
  • Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
  • Wuta ta kashe ɓarawon wayar lantarki a Jigawa
  • Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
  • NUJ Jigawa Ta Nada Wakilin Rediyon Tarayya A Matsayin Mamba Na Musamman
  • Gwamnati Kaduna Tace Zuba Jarin Da Ta Yi Na Euro Miliyan Dari Da Shadaya Zai Maganin Sufuri A Jihar
  • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ba Mutane 300 Tallafin Aikin Gona
  • Zabe Babu Hamayya: Isma’il Dutse Ya Karbi Ragamar NUJ Jigawa
  • Shugaban Kungiyar Hizbulla Ya Ce Cewa Kungiyarsa Ba Zata Taba Mika Kai Ga Bukatun HKI Ba