Ɗan wasan Manchester United, Leny Yoro da Matthijs de Ligt da kuma Ayden Heaven ba suyi atisaye ba, bayan da ƙungiyar ke shirin buga wasan karshe a Europa League da Tottenham a makon gobe.

Ranar Juma’a United za ta je Stamford Bridge domin karawa da Chelsea a Premier, amma dai hankalinta yana wasan da za ta kara ranar Laraba a birnin Bilbao.

Yoro ya ji rauni ranar Lahadi a wasan da West Ham ta doke United 2-0, shi kuwa De Light a wasan Brentford ya ji rauni.

Shi kuwa Heaven ya yi atisaye shi kaɗai, sai dai Jonny Evans da Toby Collyer sun yi atisaye tare da ƴan wasan United.

Diogo Dalot ya motsa jiki shi kaɗai, wanda ke fatan buga wasan karshen, amma dai Lisandro Martinez da Joshua Zirkzee sun gama buga wasannin kakar nan, sakamkon jinya.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wasanni

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

Mai magana da yawun ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ya bayyana a yau Talata 12 ga wata cewa, bisa dokoki ko ka’idojin da suka shafi saka wasu sassa cikin wadanda aka sanyawa takunkumin sayar musu da kayayyaki, ma’aikatar ta fitar da sanarwa mai lamba 21 da ta 22 a ranar 4 da kuma ranar 9 ga watan Afrilun bana, inda ta saka wasu sassa 28 na Amurka cikin wadanda ta sanyawa takunkumin sayar musu da kayayyaki, wato hana sayar musu kayayyakin amfanin jama’a da ake iya amfani da su a bangaren soja. Har wa yau, domin tabbatar da matsayar da aka cimma a wajen shawarwarin manyan jami’an Sin da Amurka a bangaren tattalin arziki da cinikayya, an yanke shawarar cewa, tun daga yau Talata 12 ga watan Agusta, za a ci gaba da dakatar da wannan mataki na tsawon kwanaki 90 ga sassa guda 16 na Amurka da Sin ta sanyawa takunkumin bisa sanarwar ranar 4 ga watan Afrilun bana. Sa’annan ga sassan Amurka 12 da Sin ta sanyawa takunkumin bisa sanarwar ranar 9 ga watan Afrilu, za a daina aiwatar da matakin a kan su.

 

Jami’in ma’aikatar cinikayya ta Sin ya yi karin haske cewa, idan ’yan kasuwa na bukatar fitar da kayayyaki zuwa ga wadannan sassan Amurka, ya kamata su nemi izini daga ma’aikatar cinikayya ta Sin, wadda za ta binciki batun bisa dokoki da ka’idoji, sannan a ba wadanda suka dace izini. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin aiwatar da doka na bai wa masu laifi ƙwarin guiwa — Ɗan majalisar Gombe
  • Ranar Matasa: Ciyaman ya jinjina wa gwamnatin Gombe kan ɗaukar matasa aiki
  • Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki
  • Kungiyar SSANU Ta Ba Gwamnatin Taraba Wa’adin Sati Biyu Akan Kudaden Albashin Da Ba A Biya Ba.
  • Ranar Hausa ta duniya: Za a yi gagarumin biki a fadar Sarkin Daura
  • An kama basarake kan zargin yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Gombe
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki
  • Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm