More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Duk wanda ya shekara arba’in zuwa sama ya san irin tarbiyyar da ya samu daga wurin iyayensa a da, da irin mu’amalar da ke tsakaninsa da iyaye da kuma irin shaƙuwar da ke tsakanin ’ya’ya da iyaye.

A yanzu kuwa, abubuwa sun canza daga yadda aka san su, inda abubuwa suka rincaɓe suka yi wa iyaye yawa.

Ɗaya daga cikin manyan sauyin da aka samu shi ne aikin gwamnati ko aikin wata da iyaye mata suke yi a wannan zamani wanda a wasu lokuta ke barazana ga irin kulawar da ’ya’ya suke samu.

NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya? DAGA LARABA: Ɓoyayyun Dalilan Da ke Sa Faɗuwa Jarabawa A Najeriya

Shirin Najeriya A Yau zai yi nazari ne kan irin ƙalubalen da iyaye ke fuskanta a wannan zamani wajen tarbiyyar ’ya’yansu.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: ya ya iyaye kulawa Tarbiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya

Dakarun Sojin Amurka sun kammala shirye-shiryen kai hare-hare a Najeriya bayan umarnin da Shugaba Donald Trump, ya bai wa Ma’aikatar Tsaron ƙasar kan ɗaukar mataki game da zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

Jaridar The New York Times ta ruwaito cewa rundunar sojin Amurka da ke nahiyar Afirka (AFRICOM), ta gabatar da yadda hare-haren za su kasance.

An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa

Daga cikin shirin akwai kai wa ’yan ta’adda hare-hare da jiragen yaƙi da amfani da jirage marasa matuƙa.

Sannan kuma akwai tsarin haɗin gwiwa da sojojin Najeriya ta hanyar musayar bayanan leƙen asiri da tallafin kayan aiki.

Sai dai jami’an Ma’aikatar Tsaron Amurka sun yi gargaɗin cewa irin waɗannan hare-haren ba lallai su magance matsalolin tsaro a Najeriya ba.

Sun ce dole sai an gudanar da yaƙi mai faɗi  kamar yadda aka yi a Iraƙi ko Afghanistan, sai dai sun ce hakan zai sa Amurka ta kashe maƙudan kuɗaɗe.

Trump, ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da tin sakaci wajen “kisan Kiristoci,” kuma ya bayar da umarnin dakatar da sayar wa Najeriya makamai.

Gwamnatin Najeriya ta ƙaryata zargin, inda ta danganta matsalar tsaro da wasu abubuwa kuma tana shafar kowane ɓangare na addini.

Mai bai wa Shugaba Tinubu shawara, Daniel Bwala, ya bayyana cewa Najeriya ba ta buƙatar sojojin Amurka su shiga ƙasarta, sai dai taimako a fannin leƙen asiri da kayan aiki, tare da buƙatar Amurka ta mutunta Najeriya.

Ƙasar China ta goyi bayan Najeriya, tare da gargaɗin Trump kan tsoma baki cikin harkokin da suka shafi ƙasa mai ’yanci.

Masana da tsofaffin Hafsoshin sojin Amurka sun yi gargaɗin cewa irin wannan farmaki zai iya ƙara ta’azzara matsalar tsaro.

Sun kuma bayyana cewa matsalar tsaro a Najeriya ta samo asali ne daga ’yan fashi, rikicin filaye, da ta’addanci da ke shafar Musulmai da Kiristoci baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar Najeriya
  • Barazanar Trump: Ya kamata shugabannin Najeriya su farka daga bacci — Bishop Kukah
  • Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso Rock
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)
  • Sama da gidaje 8,000 za su samu wutar lantarki daga hasken rana a Gombe
  • Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir