NAJERIYA A YAU: Ƙalubalen Da Iyaye Ke Fuskanta Wajen Tarbiyyar ’Ya’yansu
Published: 8th, May 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Duk wanda ya shekara arba’in zuwa sama ya san irin tarbiyyar da ya samu daga wurin iyayensa a da, da irin mu’amalar da ke tsakaninsa da iyaye da kuma irin shaƙuwar da ke tsakanin ’ya’ya da iyaye.
A yanzu kuwa, abubuwa sun canza daga yadda aka san su, inda abubuwa suka rincaɓe suka yi wa iyaye yawa.
Ɗaya daga cikin manyan sauyin da aka samu shi ne aikin gwamnati ko aikin wata da iyaye mata suke yi a wannan zamani wanda a wasu lokuta ke barazana ga irin kulawar da ’ya’ya suke samu.
NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya? DAGA LARABA: Ɓoyayyun Dalilan Da ke Sa Faɗuwa Jarabawa A NajeriyaShirin Najeriya A Yau zai yi nazari ne kan irin ƙalubalen da iyaye ke fuskanta a wannan zamani wajen tarbiyyar ’ya’yansu.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ya ya iyaye kulawa Tarbiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bar Abuja zuwa birnin New York na Ƙasar Amurka, domin halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya karo na 80.
Taron zai gudana daga ranar Litinin, 22 ga watan Satumba, zuwa ranar Lahadi, 28 ga watan Satumba, 2025.
Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu Jami’ar European-American ta musanta bai wa Rarara digirin girmamawaShettima zai wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wannan babban taro.
Zai gabatar da jawabi, tare da shiga muhawarar shugabannin ƙasashe a zauren taron.
A yayin taron, Mataimakin Shugaban zai kuma bayyana sabbin muradun Najeriya a ƙarƙashin yarjejeniyar kare muhalli.
Wannan zai gudana ne a wani taro na musamman kan sauyin yanayi da Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya zai shirya a ranar Laraba, 24 ga watan Satumba.
Haka kuma, Shettima zai halarci wani taron koli kan samar da gidaje masu sauƙi da sauƙin farashi, wanda Shugaban Ƙasar Kenya zai jagoranta.
Bayan kammala taron, Shettima zai wuce Birnin Frankfurt, na Ƙasar Jamus, inda zai gana da jami’an bankin Deutsche Bank kafin dawowa Najeriya.