Waji Jirgin Amurka Samfurin F-18 Na 3 Ya Fadi A Tekun “Red-Sea”
Published: 7th, May 2025 GMT
Rundunar sojan Ruwan Amurka ta sanar da cewa; Jirgin sama samfurin F-18 wanda kudinsa ya kai dalar Amurka miliyan 67 ya fadi akan jirgin dakon jiragen ruwa na ” USS Harry Truman” a tekun “Red Sea”.
Jaridar ” Washington Post” ta buga labarin dake cewa; Jirgin ta fado ne a lokacin da yake kokarin sauka akan doron jirgin ruwan dakon jiragen saman na ” USS Harry Trauman”.
Sanarwar ta kuma kara da cewa; Matuka jirgin sun fice daga cikinsa ta hanar lema, kuma an tserato da su daga cikin ruwa ta hanyar jirgi mai saukar angulu. Matukan, kamar yadda sanarwar ta sojojin na Amurka, sun ji rauni.
Wani jami’in soja wanda ya bukaci a sakaya sunansa ya fada wata kafar watsa labaru cewa; Yawan faduwar da jiragen yakin samfurin F-18 suke yi, ya ja hankalin manyan kwamandojin sojan Amurka.”
A ranar 28 ga watan Afrilu ma dai rundunar sojan ruwan Amurkan ta sanar da faduwar jirigin yakin samfurin F-18 a lokacin da yake sauka.
Bugu da kari a cikin watan Disamba na shekarar da ta wuce, wani jirgin saman ya fado ya ci karo da jirgin dakon jiragen yakin kamar yadda rundunar sojan ruwan Amurkan ta sanar.
Wasu masu bin diddigin abinda yake faruwa a yankin suna danganta fadowar jiragen saman na Amurka da hare-haren kungiyar Ansarullah ta Yemen.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu iya galaba kan Iran ko babu Amurka — Isra’ila
Shugaban Isra’ila, Isaac Herzog, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta iya samun nasara a yaƙin da take yi da Iran ko da kuwa Amurka ba ta shigar mata ba.
Sai dai Herzog ya shaida wa ABC News cewa kawar da barazanar nukiliyar Iran yana da muhimmanci ga “duniya mai ’yanci”, ciki har da Amurka.
Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — BirtaniyaDa yake amsa tambayar ko me zai ce dangane da yiwuwar shigar wa ƙasarsa yaƙin da take yi da Iran da Shugaba Donald Trump ya yi iƙirari, Herzog ya ce “ina da cikakkiyar yarda a kan duk wani hukunci da zai yanke kuma ina da tabbacin duk abin da ya yanke shi ne daidai.
Herzog ya ce mako guda ke nan da fara yaƙin amma ya tabbatar da cewa barazanar Iran ba za ta kau ba nan take.
“Babbar nasarar da za mu samu ita ce kawo ƙarshen barazanar nukiliyar Iran,” a cewar Herzog.
“[Jagoran addini na Iran, Ayotallah Ali Khamenei] shi ne kan macijin da ke jagorantar duk wata barazana da Iran take yi da muke buƙatar mu sare.
“Tun ba yanzu ba yake babatun ganin bayan ƙasarmu da al’ummarta. Saboda haka ba mu da wata manufa a yanzu face mun yi maganinsa,” kamar yadda Herzog ya shaida wa gidan talabijin na ABC.