Waji Jirgin Amurka Samfurin F-18 Na 3 Ya Fadi A Tekun “Red-Sea”
Published: 7th, May 2025 GMT
Rundunar sojan Ruwan Amurka ta sanar da cewa; Jirgin sama samfurin F-18 wanda kudinsa ya kai dalar Amurka miliyan 67 ya fadi akan jirgin dakon jiragen ruwa na ” USS Harry Truman” a tekun “Red Sea”.
Jaridar ” Washington Post” ta buga labarin dake cewa; Jirgin ta fado ne a lokacin da yake kokarin sauka akan doron jirgin ruwan dakon jiragen saman na ” USS Harry Trauman”.
Sanarwar ta kuma kara da cewa; Matuka jirgin sun fice daga cikinsa ta hanar lema, kuma an tserato da su daga cikin ruwa ta hanyar jirgi mai saukar angulu. Matukan, kamar yadda sanarwar ta sojojin na Amurka, sun ji rauni.
Wani jami’in soja wanda ya bukaci a sakaya sunansa ya fada wata kafar watsa labaru cewa; Yawan faduwar da jiragen yakin samfurin F-18 suke yi, ya ja hankalin manyan kwamandojin sojan Amurka.”
A ranar 28 ga watan Afrilu ma dai rundunar sojan ruwan Amurkan ta sanar da faduwar jirigin yakin samfurin F-18 a lokacin da yake sauka.
Bugu da kari a cikin watan Disamba na shekarar da ta wuce, wani jirgin saman ya fado ya ci karo da jirgin dakon jiragen yakin kamar yadda rundunar sojan ruwan Amurkan ta sanar.
Wasu masu bin diddigin abinda yake faruwa a yankin suna danganta fadowar jiragen saman na Amurka da hare-haren kungiyar Ansarullah ta Yemen.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar Najeriya
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Jibrin Barau, ya nemi Shugaban Amurka, Donald Trump, ya janye barazanar da ya yi wa Najeriya kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.
Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin soji a kan Najeriya saboda zargin ana zaluntar Kiristoci.
Barazanar Trump: Ya kamata shugabannin Najeriya su farka daga bacci — Bishop Kukah Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso RockBarau ya ce maganar da Trump ya yi ba ta dace ba, kuma ta saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa.
A cikin wani bidiyo da aka fitar a ranar Juma’a, Mataimakin Shugaban Majalisar, ya ce Najeriya, a matsayinta na ƙasa mai cin gashin kanta, ba za ta yadda a ci zarafinta ko a tsangwame ta ba.
“Shugaban Amurka ya fito ya ce, ‘Najeriya wulaƙantaciyyar ƙasa ce, za mu kai muku hari,’ wannan bai dace ba.
“Ya kamata ya janye wannan maganar ya kuma nemi afuwar Najeriya,” in ji Barau.
Ya ƙara da cewa maganganun Trump sun karya dokokin diflomasiyya da na ƙasa da ƙasa.
“Idan kuna da ƙorafi a kan ƙasarmu, ku bi hanyoyin shari’a. Ku je Majalisar Ɗinkin Duniya, ku nemi izini, sannan ku aiwatar da shi yadda ya dace. Tsallake wannan hanya ba abin da ya dace ba ne,” in ji shi.
Barau, ya jaddada cewa kalaman Trump ba za su firgita Najeriya ba, kuma ya kamata shugaban Amurka ya girmama ƙasa mai cin gashin kanta.
“Ba za mu ji tsoron faɗin gaskiya ba. Da Trump yana nan, da na faɗa masa kai-tsaye cewa abin da yake yi ya saɓa wa dokokin ƙasa da ƙasa kuma ba daidai ba ne,” in ji shi.