Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum
Published: 7th, May 2025 GMT
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya yi zargin cewa sojoji da sauran jami’an tsaro na bayar da gudunmawar aikata miyagun laifuka da cin zarafin jama’a a Nijeriya.
Zulum ya faɗi hakan ne yayin da yake haramta sayar da barasa a birnin Maiduguri da kewaye.
Ka-ce-na-cen da ya biyo bayan ziyarar Tinubu a Katsina DAGA LARABA: Ɓoyayyun Dalilan Da ke Sa Faɗuwa Jarabawa A NajeriyaGwamnan ya bayyana haka ne a ranar Talata a wajen ƙaddamar da wani kwamitin da aka kafa don “ƙwace haramtattun otal-otal da gidajen karuwai da gidajen kwana da maɓoyar miyagun laifuka da kuma daƙile illolin munanan ɗabi’u.
Gwamnan ya ce tsofaffin jami’an tsaron Nijeriya da na yanzu da suke aiki sun taka rawa wajen jawo jama’a cikin aikata miyagun laifuka kamar tsaurin ra’ayi da karuwanci da sauran munanan ɗabi’u, lamarin da ke kara ta’azzara barazanar ta’addanci a jihar.
“Na yi farin ciki da sanin cewa jami’an soji suna wajen nan, musamman sojoji, ‘yan sanda, da sauran su, domin yawancin waɗannan ayyukan wa ke yin su?
“Wasu daga cikinsu akwai jami’an soji da aka kora da masu ci a yanzu har da fararen hula.
“Don haka, bai kamata a ƙi sukar kowane ɓangare ba a cikin wannan lamarin idan har muna son babban birnin Maiduguri da kuma jihar ta kawar da ta’addanci da sauran laifuka,” in ji Zulum.
A takaitaccen taron, Zulum ya sake kafa kwamitin tare da sake ba wa kwamitin damar kawar da duk wani nau’i na miyagun laifuka da munanan ɗabi’u a cikin birnin Maiduguri da kewaye.
Dokar hana sayar da barasa da kayan maye, a cewar gwamnan, ta samo asali ne daga yadda ake ta samun tashe-tashen hankula a tsakanin ƙungiyoyin da ke gaba da juna da ƙungiyoyin asiri da karuwanci da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da ‘yan fashi da sata, waɗanda suka haddasa asarar rayuka da dukiya.
Gwamnan ya haɗa hannu da sojoji, ‘yan sanda, sibil difens da wasu jami’an tsaro da dama da suka haɗa da ’yan sa-kai domin shiga cikin kwamitin domin gudanar da cikakken bincike.
Da yake amincewa da aikin da ke gaban kwamitin da aka sake kafawa, shugaban kwamitin ya yi tir da tabarbarewar harkokin tsaron cikin gida a Maiduguri tare da bayyana matakin da kwamitin zai ɗauka nan take.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi Jami an Tsaro jihar Borno Miyagun Laifuka miyagun laifuka
এছাড়াও পড়ুন:
Zulum Ya Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira 6,000 Garuruwansu A Borno
“Mun rufe dukkan sansanonin ‘yan gudun hijira da ke cikin Maiduguri. Yanzu haka saura biyu da ba na hukuma ba. Mun riga mun dawo da kashi 75 na ‘yan sansanin Muna gida, saura kashi 25 za su koma cikin kwanaki masu zuwa.”
Kowane iyali sun samu tallafin abinci, kayan gini da kulawar lafiya.
Haka kuma, kowane magidanci mace ko namiji za a ba shi Naira 100,000, yayin da matan gidan za su ƙara samun Naira 50,000 don taimaka musu da buƙatunsu na yau da kullum.
Za a Ƙara Inganta Cibiyar Koyo Sana’o’i a Gidan Gyaran Hali
Tun da safiyar ranar Litinin, Gwamna Zulum ya kai ziyara gidan gyaran hali na manyan laifuka da ke Maiduguri.
Ya ce za a inganta cibiyar koyar da sana’o’i da ke gidan don taimaka wa fursunoni su koyi sana’a da za su yi amfani da ita bayan an sake su.
“Manufar ɗaure mutum a gidan gyaran hali ita ce gyara halayensa, ba wai tsare shi kawai ba. Wannan ba zai yiwu ba sai akwai kayan aikin koyarwa da ake buƙata” in ji Zulum.
“Za mu duba wasu daga cikin fursunonin da ke da ƙananan laifuka, mu gani ko akwai yiwuwar a sake su bisa doka.”
Zulum ya samu rakiyar ɗan Majalisar Tarayya, Bukar Talba, shugaban ma’aikatansa na riƙon ƙwarya, mai ba shi kan harkokin addini da wasu jami’an gwamnati.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp