Malam Bala Dutse, wanda ɗansa Amadu yana cikin waɗanda aka kashe, ya bayyana cewa gwamnati na ƙoƙarin mantawa da al’amarin.

“An ce an kama wasu, amma har yau ba mu ji komai ba. Na rasa ɗana, kuma rayuwata ta shiga taka mai wuya. Mafi ƙaranci, gwamnati ta fito ta faɗa mana abin da ke faruwa,” in ji shi cikin hawaye.

Hauwa’u Isa, matar ɗaya daga cikin waɗanda aka kashe, ta ce tana wahala da ’ya’yanta uku.

“Sun ce za su taimaka mana da adalci, amma har yau babu wani taimako. Ba zan daina fatan samun adalci ba, amma har yaushe za mu jira?” in ji ta.

Idan ba a manta ba gwamnonin Kano da Edo, Abba Kabir Yusuf da Monday Okpebholo, sun ziyarci iyalan maharban a baya, inda suka yi alƙawarin za a yi adalci da kuma ba su tallafi.

Gwamna Abba ya kafa kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam Gwarzo.

Sai dai bayan kwanaki 40, iyalan na ci gaba da kukan cewa babu wani ci gaba da aka samu.

Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Kibiya, Nasiru Adam Abdulaziz, ya ce ya fahimci halin da ake ciki, amma ya roƙi su da su yi haƙuri.

Ya tabbatar da cewa an kama wasu kuma an kai su Abuja, amma ya nemi a yi shari’a a bainar jama’a domin tabbatar da adalci.

Wannan kisa ya nuna irin matsalar rikice-rikicen ƙabilanci da ake fama da ita a Nijeriya.

Da dama na ganin cewa gwamnati na yin alƙawuran da ba ta cikawa, lamarin da ke hana mutane yarda maganganunta.

Yayin da aka yi addu’ar 40 ta mamatan, iyalansu sun ce ba za su daina nema wa ’yan’uwansu adalci ba.

“Za mu ci gaba da magana har sai an yi mana adalci,” in ji Malam Bala Dutse.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Diyya Iyalai Maharba

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro

Gwamnan Jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya bai wa ƙungiyar maharba ta ƙasa (PROHAN) reshen Gombe, kyautar motoci Hilux guda biyu da kuma babura guda biyar domin taimaka musu wajen yaƙi da ’yan ta’adda da masu garkuwa da mutane.

An miƙa wa shugaban ƙungiyar, Rabiu Baushe (Baushen Gombe) kyautar, wanda yana cikin shirin gwamnatin na ƙara bunƙasa tsaro da bayar da kyautar kayan aiki don kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

’Yan sanda sun kama mutane 5 kan zargin satar abincin yara a Borno Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu

Gwamna Inuwa ya ce: “Tsaro shi ne ginshiƙin ci gaban al’umma. Ba za mu samu ci gaba, ba tare da zaman lafiya ba.

“Gwamnatina za ta ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro da ƙungiyoyin sa-kai domin kawo ƙarshen barazanar ta’addanci.”

A nasa jawabin, Rabiu Baushe, ya gode wa gwamnan bisa wannan tallafi, inda ya bayyana cewa motocin da baburan za su ƙara musu ƙarfi wajen yin sintiri da shawo kan hare-hare a yankunan karkara.

Ya kuma yi alƙawarin cewa ƙungiyar PROHAN za ta ci gaba da haɗa kai da jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a dukkanin sassan Jihar Gombe.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu, sun sace mutum 8 a Kwara
  • Imam Khamenei: Hadin kan al’ummar Iran a yakin kwanaki 12 ya sanya makiya kunya
  • Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Tabbatar Da Adalci Ga Falasdinawa Wajen Maido Da Hakkinsu Na Kasa
  • Da Ɗumi-ɗumi: Gwamnan Ribas, Fubara Ya Ziyarci Tinubu A Fadar Gwamnati A Abuja
  • Ballon d’Or: Wa zai lashe kyautar 2025?
  • Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya
  • Ballon d’Or: ’Yan wasa 5 da ke iya lashe kyautar 2025 
  • An kashe jami’an tsaro 53 a cikin mako biyu —Bincike
  • APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027
  • Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro