Malam Bala Dutse, wanda ɗansa Amadu yana cikin waɗanda aka kashe, ya bayyana cewa gwamnati na ƙoƙarin mantawa da al’amarin.

“An ce an kama wasu, amma har yau ba mu ji komai ba. Na rasa ɗana, kuma rayuwata ta shiga taka mai wuya. Mafi ƙaranci, gwamnati ta fito ta faɗa mana abin da ke faruwa,” in ji shi cikin hawaye.

Hauwa’u Isa, matar ɗaya daga cikin waɗanda aka kashe, ta ce tana wahala da ’ya’yanta uku.

“Sun ce za su taimaka mana da adalci, amma har yau babu wani taimako. Ba zan daina fatan samun adalci ba, amma har yaushe za mu jira?” in ji ta.

Idan ba a manta ba gwamnonin Kano da Edo, Abba Kabir Yusuf da Monday Okpebholo, sun ziyarci iyalan maharban a baya, inda suka yi alƙawarin za a yi adalci da kuma ba su tallafi.

Gwamna Abba ya kafa kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam Gwarzo.

Sai dai bayan kwanaki 40, iyalan na ci gaba da kukan cewa babu wani ci gaba da aka samu.

Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Kibiya, Nasiru Adam Abdulaziz, ya ce ya fahimci halin da ake ciki, amma ya roƙi su da su yi haƙuri.

Ya tabbatar da cewa an kama wasu kuma an kai su Abuja, amma ya nemi a yi shari’a a bainar jama’a domin tabbatar da adalci.

Wannan kisa ya nuna irin matsalar rikice-rikicen ƙabilanci da ake fama da ita a Nijeriya.

Da dama na ganin cewa gwamnati na yin alƙawuran da ba ta cikawa, lamarin da ke hana mutane yarda maganganunta.

Yayin da aka yi addu’ar 40 ta mamatan, iyalansu sun ce ba za su daina nema wa ’yan’uwansu adalci ba.

“Za mu ci gaba da magana har sai an yi mana adalci,” in ji Malam Bala Dutse.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Diyya Iyalai Maharba

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen

Iran ta yi kakkausar suka da kakkausar murya kan zargin Amurka da da na Isra’ila suka cewa ta na da hannu a hare-haren ramuwar gayya na kasar Yemen.

Iran ta ce zarge zagren basu da tushe balle makama.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya fada a yammacin jiya Lahadi cewa, matakin da kasar Yemen ta dauka na goyon bayan al’ummar Falasdinu, wani mataki ne mai cin gashin kansa, wanda aka dauka a matsayin goyan bayan Palasdinawa.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya jaddada cewa, sojojin Amurka ne suka shiga yakin domin tallafawa kisan kiyashin da gwamnatin sahyoniyawa ke ci gaba da yi a zirin Gaza.

Don haka Araghchi ya soki Amurka da aikata laifukan yaki ta hanyar kai hare-hare kan ababen more rayuwa da wuraren fararen hula a garuruwan Yemen.

Araghchi ya kira hare-haren da Amurka ta kai kan kasar Yemen a matsayin cin zarafi ga kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ci gaba da cewa zargin da ake yi na baya-bayan nan wata dabara ce ta karkatar da hankali daga laifukan da gwamnatin sahyoniyawan ta ke aikatawa a Falastinu, da boye irin gazawar da Isra’ila da kawayenta suka yi a cikin dabarunta, da kuma tabbatar da ci gaba da tada zaune tsaye a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gabatar da sabbin shaidu kan Nnamdi Kanu
  • Jagora: Muhimmin Aikin Makarantar “Hauza” Shi ne Isar Da Sakon Addini
  • Ku Guji Rubuta Rahoton Farfagandar ‘Yan Ta’adda Mai Ɗaukar Hankali – Gwamnati Ga ‘Yan Jarida 
  • APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo
  • Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
  • Korar Ma’aikata: Likitocin Birnin Tarayya Sun Tsunduma Yajin Aikin Gargadi Na Kwanaki 3 
  • An kashe mutum 6 a sabon hari a Filato
  • ‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa
  • Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen