Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta
Published: 24th, April 2025 GMT
Munanan azabtarwa kan fursunonin Falasdinawa a gidajen kurkukun haramtacciyar kasar Isra’ila da suka hada da fyade da dangogin azaba
Rahoton da Hukumar Kula da Fursunoni Falasdinawa dakungiyar Fursunonin Falasdinawa da aka saka daga gidan kurkukun haramtacciyar kasar Isra’ila sun fiyar da rahoton hadin gwiwa a yau Alhamis, 24 ga watan Afrilun shekara ta 2025, da ya kunshi munanan shaida daga fursunonin Zirin Gaza da ke tsare a gidan yarin Negev da sansanin Ofer na gwamnatin haramtaciyar kasar Isra’ila.
Rahoton ya bayyana yadda ake ci gaba da yin fyade da cin zarafi ga wadanda ake tsare da su a Gaza.
Wanda ake tsare da shi a sansanin Ofer ya bayyana cewa da gangan masu gadin sansanin suke kara radadin yadda wanda ake tsare da su da hakan ke kara masifar azabtarwar da ake gana musu. Haka kuma wanda ake tsare ana yi masa fyade a gaban ’yan uwansa da ake tsare da su, da nufin wulakanta shi da kuma rusa tunaninsa, da hakan ke kara tsoro da firgici a tsakanin sauran wadanda ake tsare da su.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: da ake tsare da su
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Sai dai babu wani tabbaci daga gwamnatin Iran ko Isra’ila kan cewa sun yarda su dakatar da yaƙin.
Trump ya kira rikicin da ake ciki da suna “yaƙin kwana 12,” yana mai cewa wannan rikici da za a iya yin shekaru ana fafatawa da shi bai bazu ba, kuma ba zai bazu ba.
Mene ne ke faruwa yanzu?
Bayan da Trump ya sanar da cewa an tsagaita wuta, Isra’ila ta ce an kashe mutane uku sakamakon hare-haren da Iran ta kai.
Amma ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya ce babu wata yarjejeniya ta tsagaita wuta.
Sai dai ya ce Iran za ta daina kai hari idan Isra’ila ma ta dakatar da nata.
Rikicin ya tsananta ne bayan Iran ta kai hari sansanin sojin Amurka da ke Qatar, wanda ya sa Trump ya nemi a dakatar da faɗan.
Me Iran da Isra’ila suka ce?
Gidan talabijin na Iran (IRINN) ya ce an tsagaita wuta ne bayan da Iran ta samu nasara a harin da ta kai.
Sun ce Trump ne ya roƙi a daina faɗam.
Ministan harkokin wajen Iran ya ce Iran ta daina kai hari tun ƙarfe 4 na dare, idan har Isra’ila za ta daina nata.
Har yanzu Isra’ila ba ta fitar da wata sanarwa ba kan tsagaita wutar, sai dai bayan sanarwar Trump, Isra’ila ta sake kai hari Iran.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp