HausaTv:
2025-06-15@07:50:49 GMT

Iran ta jinjinawa Sin da Rasha a matsayin kawayenta na kut-da-kut

Published: 24th, April 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jinjinawa kasashen Sin da Rasha a matsayin abokan hulda na kut-da-kut da kasar, yayin da ya isa birnin Beijing domin yin shawarwari da manyan jami’an kasar Sin, gabanin yin tattaunawa zagaye ta uku da Amurka kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran.

Abbas Araghchi ya shaida wa kafar yada labaran Iran a babban birnin kasar Sin a ranar Laraba cewa, “Sin da Rasha abokan hulda ne na kut da kut da suka tsaya tare da mu a lokutan wahala, don yana da kyau da ma’ana mu ci gaba da tuntubar juna tare da su a bangarori daban-daban, musamman ma yanzu da ake tattaunawa da Amurka.

“Ya zama dole mu sanar da abokanmu a kasar Sin cikakken bayani game da al’amuran da ke gudana tare da tuntubarsu.” Inji shi.

Yayin da yake jaddada cewa, ya yi irin wannan ganawa da manyan jami’an kasar Rasha a birnin Moscow a makon jiya, Araghchi ya ce yana fatan samun kyakkyawar tattaunawa da mahukuntan Beijing, domin isar da sakon shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ga mahukuntan kasar Sin.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ce, “A baya kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa kuma mai ma’ana a batun nukiliyar kasar Iran, kuma ko shakka ana bukatar hakan.

Za mu ci gaba da tuntubar Sin a matsayinta na mamba a kwamitin sulhun MDD, mamba a kwamitin gudanarwar hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA, bugu da kari kawa  ta kut-da-kut ta Jamhuriyar Musulunci ta Iran, inji ministan harkokin wajen kasar ta Iran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci

Jagoran juyin musulunci na Iran wanda shi ne babban kwamandan rundunonin sojan kasar Iran, ya nada sabbin kwamandoji da maye gurbinsu da wadanda su ka yi shahada.

Bayan shahadar kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci Shahid Hussain Salami, da kuma  babban hshahid Muhammad Hussain Bakiri, sai Shahid Gulam Ali Rashid wanda shi ne kwamandan Bakirin soja na “Khatamul-Anbiya, jagoran juyin ya sanar da sunayen wadanda su ka maye gurbinsu.

Birgediya Muhammad Pakphur shi ne wanda jagoran ya sanar a matsayin sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci, sai kuma  Manjo Janar Musawi a mastayin sabon kwamandan rundunar sojan kasar, yayin da aka nada janar Ali Shadmani a matsayin kwamandan Barikin soja na Khatamul-Anbiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • An Kaddamar Da Bikin Gabatar Da Jerin Shirye-shiryen Telebijin Da Fina-finai Na CMG A Birnin Astana
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya