Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Ba su da niyyar gudanar da tattaunawa da Amurka a fili

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana ta shafinsa na Twitter a takaitaccen jawabin da aka shirya yi a taron manufofin nukiliya na kasa da kasa na Carnegie, yana mai jaddada cewa, “Iran sam ba ta da niyyar yin shawarwari da Amurka a fili a bainar jama’a.

Araghchi ya rubuta a shafinsa na Twitter da safiyar yau Talata cewa, “Lokacin da ya amince da gabatar da muhimmin jawabi a taron manufofin nukiliya na kasa da kasa na Carnegie, har yanzu Iran da Amurka ba su sanya ranar da za a yi shawarwarin zagaye na gaba ba, wanda za a fara a matakin kwararru a ranar Laraba da kuma babban mataki a ranar Asabar.

Ya kara da cewa, “Kamar yadda ya jaddada a cikin jawabinsa da ya shirya, ko kadan Iran ba ta da niyyar yin shawarwari a fili a bainar jama’a.” Araghchi ya ci gaba da cewa, “A cikin jawabinsa, ya kuma bayyana karara cewa wasu ‘kungiyoyin masu sha’awa na musamman’ na kokarin yin magudi tare da bata tsarin diflomasiyya ta hanyar bata sunan masu tattaunawan tare da yin kira ga gwamnatin Amurka da ta gabatar da bukatu mafi tsanani da girma.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita

JMI ta bayyana cewa zata yi amafani da hakkinta wanda doka ya bata na ficewa daga yarjeniyar NPT don sake farfado da takunkuman tattalin arziki na MDD a kan kasar.

Jakadan kasar Iran a MDD, Amir Saeid Iravani ne ya bayyana haka a jiya Laraba.

Kamfanin dillanbcin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Iravani yana fadar haka a wata wasika da ya rubutawa kwamitin tsaro na MDD a jiya. Ya kuma kara da cewa Iran zata yi amfani da dokokin da suka bada damar yin hakan.

Kasashen Turai guda Uku jamusa Farana da Burtania suna son su yi amfani da damar da ake kira snap back don sake farfado da takunkuman MDD a kan kasar na yarjeniyar JCPOA.

Ya kammala da cewa yarjeniyar JCPOA bata da amfanmi bayan da suka kauracewa yin aiki da ita na shekaru.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar