Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam Ta Amnesty International Ta Ce; Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ba Ta Dace Da Bincike Laifukan Sojojinta Ba
Published: 21st, April 2025 GMT
Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Amnesty International ta bayyana cewa: Gwamnatin Mamayar Isra’ila ta tabbatar da cewa ba za a amince da ita ba a duk wani bincike laifukan sojojinta
Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International ta tabbatar da cewa: Gwamnatin mamayar Isra’ila ta sake tabbatar da rashin sahihancinta wajen binciken laifukan da sojojinta suka aikata.
A yayin da take tsokaci kan binciken da gwamnatin mamayar Isra’ila ke yi kan harin da aka kaiwa ma’aikatan jinya a Gaza, kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta ce a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin, 21 ga watan Afrilun wannan shekara ta 2025: Akwai zabi daya tilo na yin adalci, ta hanyar kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ko kuma kotun duniya.
Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International ta bukaci a gudanar da bincike kan wadanda ke da alhakin aikata laifukan da aka aikata cikin watanni 18 da suka gabata a Zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp