Leadership News Hausa:
2025-06-26@12:05:56 GMT

Yadda Za Ku Hada ‘Mimi Fankek’

Published: 19th, April 2025 GMT

Yadda Za Ku Hada ‘Mimi Fankek’

Yadda za ku hada:

Idan kuka samu filawa kamar kofi daya, sai suga kamar babban cokali biyu, sai gishiri kadan haka, sai baikin fauda rabin babban cokali , baikin soda rabin babban cokali, kwai daya, sai mai babban cokali biyu, madara rabin kofi.

Sai ki tankade filawar sannan ki zuba suga ki zuba gishiri baikin fauda ki zuba duk kayan da na ambata sai ki cakuda su gaba daya, ki dame su sosai, sannan ki dora firayin fan dinki idan ya danyi zafi sai ki fara zubawa daidai fadin da kike so, sannan za ki iya yi mishi dan kunne haka a sama zai dauki hankalin yara, amma za ki rage wuta ne sosai saboda shi baya son wuta, idan wuta ta yi masa yawa zai kone.

Yadda za ki gane kasan fankek din ya yi za ki ga ya dan bubbule a sama, wanda hakan alama ce ta kasan ya yi, sai ki juya shi saboda saman ma ya yi.

Za ki iya shan sa da shayi lokacin karin kumullo, ko kuma za ki iya sha da lemo da duk dai abin da kike so ko haka ma ana ci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

Rigimar shugabanci a jam’iyyar adawa ta PDP, ta lafa yayin da Sanata Samuel Anyanwu ya samu umarnin komawa bakin aikinsa a matsayin sakataren jam’iyyar na ƙasa.

Muƙaddashin shugaban jam’iyyar na ƙasa, Ambasada Umar Damagum, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Laraba a hedikwatar jam’iyyar da ke Wadata Plaza, Abuja.

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

Damagum ya kuma bayyana cewa an soke taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) karo na 100 da aka shirya yi, saboda wasu matsaloli.

Maimakon haka, jam’iyyar za ta gudanar da wani taro a ranar 30 ga watan  Yuni, wanda shi ne ranar da aka fara tsara babban taron nata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja
  • NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin Su
  • Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
  • PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta
  • Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump
  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3
  • Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
  • Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka
  • EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2