Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Garambawul A Fannin Kiwon Lafiya
Published: 17th, April 2025 GMT
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya sake jaddada kudurin gwamnatinsa na yin garambawul a fannin kiwon lafiya ta hanyar sanya tubalin gina sabbin cibiyoyin lafiya guda uku, da suka hada da Cibiyar Gwaji ta zamani, da Cibiyar kula da lafiyar Zuciya, da cibiyar samar da iskar numfashi (Cryo-Oxygen Plant) a Fanisau, da ke Dutse, babban birnin jihar.
Wadannan ayyuka, wadanda za su ci biliyoyin nairori, wani bangare ne na hangen nesan gwamnatin na mayar da Dutse cibiyar yawon bude ido kan kiwon lafiya a yankin.
A yayin bikin, Gwamna Namadi ya bayyana cewa wannan rana ta shiga kundin tarihi a ci gaban jihar.
Ya bayyana cewa an tsara wadannan cibiyoyin ne domin kara karfin jihar wajen samar da ingantaccen kula da lafiya da rage dogaro da wasu jihohi ko kasashen waje, domin neman lafiya.
Namadi ya bayyana wasu daga cikin nasarorin da gwamnatinsa ta samu da suka hada da shigar da mutane masu bukata ta musamman sama da dubu 143 cikin shirin inshorar lafiyar al’umma, da kuma farfado da asibitocin matakin farko da na biyu.
Malam Namadi ya bayyana cewa kudin farko zai fito ne daga baitul malin jihar, amma a tsawon lokaci, ana shirin tafiyar da cibiyoyin a karkashin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zaman kansu (PPP).
Ya ce wannan tsari zai tabbatar da dorewa mai inganci, tare da kawar da bukatar tafiye-tafiye zuwa wasu jihohi domin yin gwaje gwaje kamar su MRI da ke nuna hoton jikin mutum baki daya da kuma cutar da ke damunsa da kuma yin gwajin cutar sankarar Mama wato mammography.
Malam Namadi ya ce masana’antar samar da iskar numfashi ta Cryo-Oxygen za ta rika samar da kashi 100 bisa 100 na iskar oxygen mai tsafta don asibitoci, da kuma na nitrogen don amfani a masana’antar takin zamani a Najeriya.
Gwamnan ya kuma yi bayanin wasu ayyuka da ake yi a fannin lafiya da suka hada da asibitin kashi na Gumel, da asibitocin kwararru a Hadejia da Kazaure, da kuma fadada ayyukan wanke koda kyauta.
Ya bayyana cewa gwamnati ta amince da bayar da magani kyauta ga masu ciwon siga, da hawan jini, da masu cutar sikila.
Dangane da inganta ma’aikata, Gwamna Namadi ya sanar da daukar ma’aikatan lafiya sama da 920 a matakin farko, da ma’aikatan jinya 200, tare da na wucin gadi 1,000.
Ya bukaci ma’aikatan lafiya da su nuna kishi da sadaukarwa, inda ya gargadi cewa ba za lamunci sakaci da aiki da rashin da’a ba.
Gwamnan ya kuma yaba wa manyan abokan cigaban jihar kamar su UNICEF, WHO, USAID, FCDO, da gidauniyar Bill & Melinda Gates, tare da shugabannin gargajiya da na addini bisa goyon bayan da suke ci gaba da bayarwa wajen wayar da kan jama’a a fannin lafiya a fadin Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa ya bayyana cewa Ya bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Daraktar Hukumar IAEA Ya Ce: Suna Tuntubar Juna Da Iran Kuma Masu Bincikensu Sun Kamo Kasar
Darakta Janar na Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya {IAEA} ya bayyana cewa: Suna tuntubar Tehran kuma masu binciken hukumar sun koma kasar ta Iran
Darakta Janar na Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA), Rafael Grossi, ya tabbatar da komawar masu binciken Hukumarsa ta IAEA zuwa Iran da kuma ci gaba da duba wasu wurare da ba su lalace ba. Ya lura cewa yana ci gaba da tuntuɓar mahukuntan Iran kuma ya yi kira da a ƙara haɗin gwiwa don ci gaba da duba cikakkun bayanai, musamman a wuraren da aka kai hare-haren soji a kwanan nan.
A cikin rahotonsa ga kwamitin Gwamnonin a taronsu na yau da kullun, Grossi ya bayyana cewa masu binciken Hukumar IAEA sun koma Iran kuma sun gudanar da bincike a wuraren da hare-haren soji ba su shafa ba a watan Yunin da ya gabata.
Ya bayyana cewa duk da wannan ci gaba, sake ci gaba da bincike mai zurfi a wuraren da suka lalace yana buƙatar ƙarin haɗin gwiwa daga Iran don tabbatar da bin yarjejeniyar kariya.
Ya kuma ambaci sanya hannu kan “Yarjejeniyar Alkahira” tare da Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araqchi a ranar 9 ga Satumba, 2015, don kafa hanyoyin dubawa, bayyanawa, da aiwatar da kariya bayan hare-haren. Ya ƙara da cewa Iran ta sauƙaƙa wa Hukumar IAEA damar shiga wuraren da ba su lalace ba tare da sanarwa a baya, matakin da Hukumar ta yi maraba da shi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta A Gaza Kusan Sau 400 November 19, 2025 Kotu A Gabon Ta Yanke Hukuncin Dauri A Kurkuku Kan Jami’an Tsohuwar Gwamnatin Kasar November 19, 2025 Kasar Maziko Tayi Watsi Da Shirin Trump Na Kai Harin Soji Kan Iyakar Kasar. November 19, 2025 Iran Ta yi Gargadi Kan Kada Kudurin Amurka Da MDD Ta Amince Da Shi Ya Tauye Hakkin Falasdinawa November 19, 2025 kungiyar Hadin Guiwa Ta SCO Ta yi Watsi Da Adawar Da Kasashen Turai Ke Nuna wa Kasar Iran November 19, 2025 Majalisa wakilai A Najeriya Ta Bukaci Gwamnati Ta Sake Dabarun Yaki Da Ta’addanci November 19, 2025 Kimanin Falasdinawa 22 Ne Suka yi Shahada Sakamakon Harin Isra’ila A Ainul Hilwa November 19, 2025 Iran : Dole ne kudirin Amurka ya kare hakkin Falasdinawa da samuwar kasar Falasdinu November 19, 2025 Saudiyya za ta kara hannun jarinta a Amurka zuwa dala tiriliyan daya November 19, 2025 Iraki : Jam’iyyar al-Soudani ta samu rinjaye a Majalisar dokoki November 19, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci