Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-21@21:14:13 GMT

Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Garambawul A Fannin Kiwon Lafiya

Published: 17th, April 2025 GMT

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya sake jaddada kudurin gwamnatinsa na yin garambawul a fannin kiwon lafiya ta hanyar sanya tubalin gina sabbin cibiyoyin lafiya guda uku, da suka hada da Cibiyar Gwaji ta zamani, da Cibiyar kula da lafiyar Zuciya, da cibiyar samar da iskar numfashi  (Cryo-Oxygen Plant) a Fanisau, da ke Dutse, babban birnin jihar.

Wadannan ayyuka, wadanda za su ci biliyoyin nairori, wani bangare ne na hangen nesan gwamnatin na mayar da Dutse cibiyar yawon bude ido kan kiwon lafiya a yankin.

A yayin bikin, Gwamna Namadi ya bayyana cewa wannan rana ta shiga kundin tarihi a ci gaban jihar.

Ya bayyana cewa an tsara wadannan cibiyoyin ne domin kara karfin jihar wajen samar da ingantaccen kula da lafiya da rage dogaro da wasu jihohi ko kasashen waje, domin neman lafiya.

 

Namadi ya bayyana wasu daga cikin nasarorin da gwamnatinsa ta samu da suka hada da shigar da  mutane masu bukata ta musamman sama da dubu 143 cikin shirin inshorar lafiyar al’umma, da kuma farfado da asibitocin matakin farko da na biyu.

Malam Namadi ya bayyana cewa kudin farko zai fito ne daga baitul malin jihar, amma a tsawon lokaci, ana shirin tafiyar da cibiyoyin a karkashin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zaman kansu (PPP).

Ya ce wannan tsari zai tabbatar da dorewa mai inganci, tare da kawar da bukatar tafiye-tafiye zuwa wasu jihohi domin yin gwaje gwaje kamar su MRI da ke nuna hoton jikin mutum baki daya da kuma cutar da ke damunsa da kuma yin gwajin cutar sankarar Mama wato mammography.

Malam Namadi ya ce masana’antar samar da iskar numfashi ta Cryo-Oxygen za ta rika samar da kashi 100 bisa 100 na iskar oxygen mai tsafta don asibitoci, da kuma na  nitrogen don amfani a masana’antar takin zamani a Najeriya.

Gwamnan ya kuma yi bayanin wasu ayyuka da ake yi a fannin lafiya da suka hada da asibitin kashi na Gumel, da asibitocin kwararru a Hadejia da Kazaure, da kuma fadada ayyukan wanke koda kyauta.

Ya bayyana cewa gwamnati ta amince da bayar da magani kyauta ga masu ciwon siga, da hawan jini, da masu cutar sikila.

Dangane da inganta ma’aikata, Gwamna Namadi ya sanar da daukar ma’aikatan lafiya sama da 920 a matakin farko, da ma’aikatan jinya 200, tare da na wucin gadi 1,000.

Ya bukaci ma’aikatan lafiya da su nuna kishi da sadaukarwa, inda ya gargadi cewa ba za  lamunci sakaci da aiki da rashin da’a ba.

Gwamnan ya kuma yaba wa manyan abokan cigaban jihar kamar su UNICEF, WHO, USAID, FCDO, da gidauniyar Bill & Melinda Gates, tare da shugabannin gargajiya da na addini bisa goyon bayan da suke ci gaba da bayarwa wajen wayar da kan jama’a a fannin lafiya a fadin Jihar Jigawa.

Usman Muhammad Zaria 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa ya bayyana cewa Ya bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Kwara Ta Kafa Tutar Hadin Kai Mai Mita 70 A Ilorin

Gwamnatin jihar Kwara ta kafa tutar hadin kai mai tsayin mita 70 a hukumance, wanda ke zama alamar “hadin kan kasa, tafiya tare da buri a matsayin al’umma”.

 

Da yake jawabi a wani takaitaccen biki a Ilorin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya ce jihar ba ta daga tuta kawai ba, a’a tana nuna kwarin guiwar wata alama ce ta hadin kai, alfahari, da kuma kishin kasa.

 

Gwamnan ya samu wakilcin kwamishinan sadarwa na jihar Bola Olukoju, wanda wasu kwamishinoni uku suka taimaka masa: Aliyu Kora Sabi (sufuri); Nafisat Buge (Muhalli); da Nnafatima Imam (ci gaban al’umma) da sauran manyan baki.

 

A cewarsa, sandar tuta na kara karfafa martabar jihar a matsayin cibiyar kirkire-kirkire, al’adu, da jagoranci mai ma’ana.

 

Gwamna Abdulrazaq ya yi bayanin cewa, alamar za ta zama babban abin jan hankali, jawo masu ziyara, da samar da damammaki, da kuma baje kolin dabarun saka hannun jari na jihar kan ababen more rayuwa da ba wai kawai a yi amfani da su ba har ma da karfafa gwiwa.

 

Ya ce gwamnatinsa ta gina tituna, asibitoci na zamani, da karfafa samar da ruwan sha tare da bayar da tallafi ga manoma, ‘yan kasuwa, da kuma bangarori daban-daban na al’umma.

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin ZamfaraBabu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Jihar Jigawa Za Ta Sayi Motoci 36 Ga Mambobin Kungiyar NURTW
  • Kwara Ta Kafa Tutar Hadin Kai Mai Mita 70 A Ilorin
  • Tattaunawar Iran da Amurka na inganta zaman lafiya a yankin : Araghchi
  • Uwargidar Gwamnan Zamfara Ta Sake Jaddada Kudurin Dakile Tu’ammali Da Miyagun Kwayoyi A Jihar
  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su
  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnati da watsi da su a Jigawa
  • Cututtukan Da Ba Sa Yaduwa Sun Kai Kashi 30% Na Mace-Mace A Najeriya – Cappa