Haka kuma a ƙaramar hukumar Ringim ta Jihar Jigawa, ya amsa cewa ya kashe wani mutum sannan ya sayar da babur ɗinsa wanda ya sace a kan kuɗi Naira 300,000.

Rundunar ‘yansanda ta ce yanzu haka suna ci gaba da bincike a kansa a Sashen Binciken Manyan Laifuka (CID), don tabbatar da gaskiyar iƙirarin da ya yi da kuma gano ko akwai wasu da suke tare da shi.

Kwamishinan ‘yansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, ya yaba da matakin da Umar ya ɗauka na miƙa kansa, tare da kira ga sauran masu laifi da su kwaikwayi irin wannan mataki.

Ya kuma tabbatar da cewa rundunar ‘yansandan za ta ci gaba da ƙoƙari wajen kawar da masu aikata laifi a faɗin jihar.

‘Yansanda sun buƙaci jama’a da su ci gaba da bayar da haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda Ƙwace Waya

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Abba ya kafa runduna ta musamman da za ta ke tsaron tashoshin mota a Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da kafa wata runduna ta musamman da za ta ke tsaro a tashoshin mota da sauran wuraren jama’a a faɗin jihar.

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne, ya bayyana hakan cikim wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi.

Hukumar Film ta kasa ta horar da marubuta 53 rubutun fim An kashe mai ciki da ɗanta a Kano

Sanarwar ta ce wannan mataki wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin na daƙile laifuka da kuma kare jihar, musamman manyan hanyoyin shiga da fita na birnin Kano.

An bayyana cewa tashoshin mota na daga cikin wuraren da ake fuskantar barazanar tsaro saboda yawan zirga-zirgar mutane.

Rundunar ta musamman za ta mayar da hankali kan sanya ido, tattara bayanan sirri da gudanar da ayyukan tsaro tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro a tashoshin mota da sauran wurare a jihar.

Haka kuma za ta kula da wurare kamar gidajen mai da sauran wuraren da mutane ke taruwa.

Gwamna Abba, ya ce wannan mataki na nufin daƙile barazanar tsaro, inganta haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, da kuma dawo tabbatar da kwanciyar hankali a jihar.

Ya ƙara da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba mara wa hukumomin tsaro baya wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Abba ya kafa runduna ta musamman da za ta ke tsaron tashoshin mota a Kano
  • An kashe mai ciki da ɗanta a Kano
  • Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano
  • Farfesa na Farko a fannin Ilimi a Arewa, Adamu Baikie, ya rasu yana da shekara 94
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Iran Ta soki Kasashe Masu Karfi Na Bawa Isra’ila Dama Ta Musamman Wajen Kai Hare-hare
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman