Matashin Da Ya Ƙware Wajen Kashe Mutane Da Ƙwace Ya Miƙa Kansa Ga ‘Yansanda A Kano
Published: 16th, April 2025 GMT
Haka kuma a ƙaramar hukumar Ringim ta Jihar Jigawa, ya amsa cewa ya kashe wani mutum sannan ya sayar da babur ɗinsa wanda ya sace a kan kuɗi Naira 300,000.
Rundunar ‘yansanda ta ce yanzu haka suna ci gaba da bincike a kansa a Sashen Binciken Manyan Laifuka (CID), don tabbatar da gaskiyar iƙirarin da ya yi da kuma gano ko akwai wasu da suke tare da shi.
Kwamishinan ‘yansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, ya yaba da matakin da Umar ya ɗauka na miƙa kansa, tare da kira ga sauran masu laifi da su kwaikwayi irin wannan mataki.
Ya kuma tabbatar da cewa rundunar ‘yansandan za ta ci gaba da ƙoƙari wajen kawar da masu aikata laifi a faɗin jihar.
‘Yansanda sun buƙaci jama’a da su ci gaba da bayar da haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen tabbatar da tsaro a jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yansanda Ƙwace Waya
এছাড়াও পড়ুন:
Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya buƙaci Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, da ya daina siyasantar da harkar tsaro a jihar.
Ya ce kamata ya yi gwamnan ya mayar da hankali kan matsalolin da ke damun jihar.
Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankaliBarau, ya yi wannan bayani ne bayan gwamnatin Kano ta zarge shi da yin magana inda ya nemi gwamnatin ta mayar da hankali kan tsaro.
Ya ce matsalolin tsaro a ƙasar nan, ciki har da hare-haren ’yan bindiga a wasu yankunan Kano, suna buƙatar haɗin kai daga kowa.
A cikin wata sanarwa daga mai taimaka masa, Ismail Mudashiru, ya fitar, Barau ya ce zargin gwamnatin ba gaskiya ba ne.
Ya ƙalubalanci gwamnatin ta nuna bidiyon da ya yi maganar da za ta iya haddasa matsalar tsaro.
Ya ce wannan zargi ƙarya ne kuma na da nufin ɓata masa suna.
Ya ƙara da cewa bai taɓa yin wata magana da za ta kawo tangarɗa ga harkar tsaro ba.
A maimakon haka, ya ce yana aiki tare da sauran jami’ai domin inganta tsaro a Kano da sauran sassan Najeriya.
Barau, wanda shi ne Mataimakin Kakakin ECOWAS, ya buƙaci Gwamna Abba da ya “farka daga bacci” ya jagoranci jihar yadda ya kamata.
Ya ce a baya Kano na gogayya da Legas wajen ci gaba, amma rashin kyakkyawan shugabanci ya janyo mata koma baya.
Ya ce ya bai wa rundunonin ’yan sanda motocin aiki, ya bai wa jami’an ’yan sanda babura a Kano ta Arewa, sannan ya gyara wasu sassan hedikwatar ’yan sanda ta Kano.
Haka kuma, ya gina ofisoshin ’yan sanda a wurare daban-daban, ya tallafa wa hukumar DSS, sannan ya taimaka wajen kafa makarantu na horar da jami’an NSCDC, Hukumar Ayyukan ’Yan Sanda, da Hukumar Shige da Fice a wasu yankunan Kano.
Ya ce ya sanya fitilu masu amfani da hasken rana a yankinsa domin taimaka wa zirga-zirga da daddare.
A cewarsa, waɗannan ayyukan suna nuna irin gudunmawar da yake bayarwa wajen inganta tsaro, don haka ya kamata gwamnatin jihar ta yi koyi da shi maimakon ɓata masa suna.