Haka kuma a ƙaramar hukumar Ringim ta Jihar Jigawa, ya amsa cewa ya kashe wani mutum sannan ya sayar da babur ɗinsa wanda ya sace a kan kuɗi Naira 300,000.

Rundunar ‘yansanda ta ce yanzu haka suna ci gaba da bincike a kansa a Sashen Binciken Manyan Laifuka (CID), don tabbatar da gaskiyar iƙirarin da ya yi da kuma gano ko akwai wasu da suke tare da shi.

Kwamishinan ‘yansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, ya yaba da matakin da Umar ya ɗauka na miƙa kansa, tare da kira ga sauran masu laifi da su kwaikwayi irin wannan mataki.

Ya kuma tabbatar da cewa rundunar ‘yansandan za ta ci gaba da ƙoƙari wajen kawar da masu aikata laifi a faɗin jihar.

‘Yansanda sun buƙaci jama’a da su ci gaba da bayar da haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda Ƙwace Waya

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

Sanarwar ta ce: “Sauya wurin da aka yi wa fursuna Malam Abduljabbar Nasiru Kabara zuwa daya daga cikin cibiyoyin tsarewa da ke karkashin ikon tarayya hanya ce ta gudanar da aiki ta yau da kullum wacce aka yi bisa ga dokokin aiki da ka’idojin hukumar.”

 

Ta kara da bayanin cewa motsa fursunoni daga cibiyar tsarewa zuwa wata musamman wadanda ke da matakan tsaro daban-daban na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya dora wa hukumar domin tabbatar da ingantaccen tafiyar da fursunoni, gyarawa da kuma dawo da su kan turba.

 

Sanarwar ta kara da cewa: “Canjawa ko sauya wurin fursuna zuwa wata cibiyar gyaran hali mai matakin tsaro daban da wacce ake tsare da shi a baya na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya ba Hukumar Kula da Gidajen Yari, kamar yadda Dokar Hukumar ta 2019 ta tanada.”

 

Sanarwar ta ce: “Ana yanke irin wadannan shawara ne bisa la’akari da abubuwa da dama, ciki har da tsaro, tsarin rarraba fursunoni, samun wurin da ya dace a cibiyoyi, da kuma bukatun gyarawa da farfado da fursuna.”

 

CSC Musbahu ya tabbatar wa jama’a cewa duk da wannan sauya wuri, ana ci gaba da kiyaye dukkan hakkokin Malam Abduljabbar.

 

Ya ce: “An tabbatar wa jama’a cewa walwala da dukkan hakkokin shari’a na Malam Abduljabbar suna nan daram karkashin kariyar doka.”

 

Sanarwar ta kara da cewa: “Wannan sauya wuri ba ya shafar matsayinsa na shari’a, hakkinsa na daukaka kara ko samun damar tuntubar lauyansa.”

 

Jami’in hulda da jama’a ya sake jaddada kudirin hukumar na tabbatar da tsare fursunoni cikin aminci, gyarawa da farfado da su, domin tabbatar da tsaron jiha da kare rayukan jama’a.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Rahotonni Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya October 17, 2025 Manyan Labarai Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn October 17, 2025 Manyan Labarai Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja October 17, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja
  • Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul
  • Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja
  • Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata
  • Jigawa Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 6 Don Bunkasa Noma, Ilimi Da Kasuwanci
  • Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma
  • Masu Bincike Na Sin Sun Kera Wani Dan Karamin Mutum Mutumin Hannu Da Zai Taimaka Wajen Gwaje-wajen Kimiyya
  • Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi
  • Duk da yarjejeniyar tsagaita wuta, Isra’ila ta kashe Falasdinawa 3 a Gaza
  • Jihar Kwara Zata Haɗin Kai Da Masu Ruwa Da Tsaki Wajen Horas Da Matasa Fasahar AI