Haka kuma a ƙaramar hukumar Ringim ta Jihar Jigawa, ya amsa cewa ya kashe wani mutum sannan ya sayar da babur ɗinsa wanda ya sace a kan kuɗi Naira 300,000.

Rundunar ‘yansanda ta ce yanzu haka suna ci gaba da bincike a kansa a Sashen Binciken Manyan Laifuka (CID), don tabbatar da gaskiyar iƙirarin da ya yi da kuma gano ko akwai wasu da suke tare da shi.

Kwamishinan ‘yansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, ya yaba da matakin da Umar ya ɗauka na miƙa kansa, tare da kira ga sauran masu laifi da su kwaikwayi irin wannan mataki.

Ya kuma tabbatar da cewa rundunar ‘yansandan za ta ci gaba da ƙoƙari wajen kawar da masu aikata laifi a faɗin jihar.

‘Yansanda sun buƙaci jama’a da su ci gaba da bayar da haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen tabbatar da tsaro a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda Ƙwace Waya

এছাড়াও পড়ুন:

Mangal ya bayar tallafin N80m don yi wa marasa lafiya tiyata a Katsina

Fitaccen ɗan kasuwar nan, Alhaji Dahiru Bara’u Mangal, ya bayar da tallafin Naira miliyan 80 don taimaka wa mutane masu fama da cutar mafitsara da matsalar gwaiwa domin yi musu tiyata kyauta.

An gudanar da tantance marasa lafiyar a Asibitin Ƙashi na Amadi Rimi kafin a fara aikin tiyatar a ranar Asabar da ta gabata.

Kebbi: PDP za ta yi haɗaka don ƙalubalantar APC a zaɓen 2027 Mutanen Sakkwato na neman ɗaukin gwamnati game da Bello Turji

Alhaji Kabir Husaini, wanda ke jagorantar aikin, ya bayyana cewa wannan shi ne karo na uku da Mangal ke bayar da irin wannan taimako ga marasa lafiya masu ƙaramin ƙarfi.

Ya ce a baya, Mangal ya taimaka wajen yi wa masu lalurar gwaiwa tiyata.

Tun bayan fara shirin a shekarun baya, sama da mutum 3,000 ne suka ci gajiyar aikin tiyatar da aka gudanar a wurare daban-daban.

A wannan karon, Mangal ya bayar da Naira miliyan 20 daga cikin tallafin domin yi wa mutum 100 tiyata a kan cutar mafitsara da kuma lalurar gwaiwa.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka ci gajiyar shirin, Adamu Aliyu, ya ce da babu wannan tallafi, da har yanzu yana fama da cutar saboda ba shi da isasshen kuɗi don biyan kuɗin tiyatar.

Alhaji Mangal ya fara bayar da irin wannan taimako tun shekarar 2016, kuma tallafin yana zuwa har wasu maƙwabtan jihohi da ma Jamhuriyar Nijar.

Wata mata da ta nemi a sakaya sunanta ta ce wannan aiki ya zama darasi ga masu hali da ba sa son taimakon jama’a.

“Tun sama da shekara 20 Alhaji Mangal ke ciyar da marasa ƙarfi da abinci, kuma har yanzu bai fasa ba,” in ji ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa
  • An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
  • An Kashe Kusan Mutane 1500 Kan Sabanin Mazhaba A Kasar Siriya A Wata Guda
  • Labari Mai Daɗi: Asibitin Kwararru Mai Zaman Kansa A Kano Ya Rage Kaso 50 Na kuɗaɗen Ayyukansu 
  • Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  • Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4
  • Mangal ya bayar tallafin N80m don yi wa marasa lafiya tiyata a Katsina
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Al’ummar Iran Masu Juriya Za Su Tsaya Tsayin Daka Waje Kare Hakkinsu
  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100