HausaTv:
2025-05-21@20:08:31 GMT

Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa

Published: 16th, April 2025 GMT

Gwamnatin Amurka ta amince da shirin mikawa HKI dubban boma-bomai saboda kashe falasdinawa a Gaza.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, sojojin HKI suna jiran isowar boma-bomai daga kasar Amurka don fara wani aikin soje na musamman a Gaza. Saboda kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.

Wata majiyar HKI, yahudawa ta fadawa kamfanin dillancin labaran ‘Ynetnews’ kan cewa sojojin sama na HKI su na dakon isowar boma-bomai har 3000 daga kasar Amurka a cikin yan makonni masu zuwa.

Labarin ya kara da cewa rundunar ta na son ta gudanar da ayyukan soje mai fadin gaske a kan Falasdinwa wanda ya zai kawo karshen Hamas ya kuma kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.

Labarin ya kara da cewa gwamnatin kasar Amurka ta na shirin aiko da wani karin boma –bomai har 10,000 nan gaba. Yahuda zasu yi amfani da wadannan boma-boman don fadada ayyukansu a yankin, wadanda suka hada da Siriya da Lebanon da kuma ita Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Fatan Tattaunawar Kasarsa Da Amurka Ta Cimma Yarjejeniya Ta Gaskiya

Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Yana fatan tattaunawar da ake yi tsakanin Iran da Amurka za ta kai ga cimma yarjejeniya ta gaskiya

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshgan ya bayyana cewa: Iran tana fatan tattaunawarta da Amurka za ta kai ga cimma yarjejeniya ta gaskiya da za ta tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.

A yammacin jiya Lahadi, a gefen taron dandalin tattaunawa na Tehran na shekara ta 2025, a wata ganawa da ministan harkokin wajen masarautar Oman Badar bin Abdullah al-Busaidi, Shugaba Pezeshkian ya yaba da irin kyakkyawar dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da kuma irin rawar da gwamnatin Oman take takawa wajen daukar nauyin shawarwarin da ba na kai tsaye ba tsakanin Amurka da Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Yana mai cewa: “Suna fatan sakamakon kokari da kuma sahihan manufofin Sultan Haitham bin Tariq, wadannan shawarwarin za su kai ga cimma yarjejeniyar adalci da za ta tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.”

Shugaban na Iran ya jaddada wajabcin kara samun kusanci a tsakanin kasashen musulmi, yana mai cewa “masu kusanci da juna da fadada hadin gwiwarsu, haka nan masu fatan cutar da al’ummar musulmi za su zama masu haifar da sabani da rabuwar kai a tsakaninsu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wasu Yahudawa Sun Hana Kayakin Agaji Shiga Yankin Gaza
  • Sara Da Sassaka Ba Ya Hana Gamji Toho
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Ya Ce; Gwamnatin Siriya Zata Iya Rugujewa Cikin ‘Yan Makonni
  • Sarkin Yawa Ya Fi Sarkin Karfi
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa ‘Yan Gudun Hijira A Lokacin Da Suke Bacci
  • Gwamnatin Kasar Masar Tana Shirye-Shiryen Sanya Kafar Wando Daya Da Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya
  • Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON
  • HKI Ta Bude Kofofin Shigar Kayakin Agaji Zuwa Cikin Gaza A Karon Farko Bayan Kimani Watanni 2.5
  • Iran Ta Ce Gabatar Da Bukatar Dakatar Da Tashe Makamashin Uranium Karshen Tattaunawar Da Amurka
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Fatan Tattaunawar Kasarsa Da Amurka Ta Cimma Yarjejeniya Ta Gaskiya