HausaTv:
2025-12-10@12:08:12 GMT

Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa

Published: 16th, April 2025 GMT

Gwamnatin Amurka ta amince da shirin mikawa HKI dubban boma-bomai saboda kashe falasdinawa a Gaza.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, sojojin HKI suna jiran isowar boma-bomai daga kasar Amurka don fara wani aikin soje na musamman a Gaza. Saboda kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.

Wata majiyar HKI, yahudawa ta fadawa kamfanin dillancin labaran ‘Ynetnews’ kan cewa sojojin sama na HKI su na dakon isowar boma-bomai har 3000 daga kasar Amurka a cikin yan makonni masu zuwa.

Labarin ya kara da cewa rundunar ta na son ta gudanar da ayyukan soje mai fadin gaske a kan Falasdinwa wanda ya zai kawo karshen Hamas ya kuma kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.

Labarin ya kara da cewa gwamnatin kasar Amurka ta na shirin aiko da wani karin boma –bomai har 10,000 nan gaba. Yahuda zasu yi amfani da wadannan boma-boman don fadada ayyukansu a yankin, wadanda suka hada da Siriya da Lebanon da kuma ita Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin

Majalisar Dattawa a ranar Talata ta amince da bukatar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin domin tabbatar da dimokuradiyya a kasar.

Majalisar ta kuma ce tana goyon bayan matakin da shugaban ya ɗauka kwanaki kafin haka domin hana yunƙurin kifar da tsarin dimokuraɗiyya a makwabciyar kasar.

Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta

Bukatar dai na kunshe ne a cikin wata wasiƙa da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio, ya karanta a zauren majalisa yayin zamanta.

Tinubu ya umarci tura sojojin makon da ya gabata domin dakile yunƙurin karɓar mulki ba bisa ka’ida ba a Jamhuriyar Benin da kuma kaucewa rikicewar tsaro a yankin yammacin Afirka.

Sai dai Tinubu bai nemi amincewar majalisa ba kamar yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

Bayan karanta wasiƙar, majalisar ta koma zaman kwamiti domin tantance bukatar. A yayin zaman, ’yan majalisa sun tattauna kan tasirin tsaro, jin‑ƙai da diflomasiyya da ke tattare da wannan mataki.

Babbar damuwar a cewarsu ta haɗa da yiwuwar kwararar ’yan gudun hijira zuwa Najeriya, tsaron iyaka da kuma tasirin matakin ga zaman lafiya da tsaro a yankin.

Bayan doguwar muhawara, majalisar ta koma zama a zaurenta, inda ta kada kuri’ar amincewa da matakin shugaban ƙasa cikin rinjaye.

Shugaban Majalisar, Akpabio, ya gabatar da rahoton kwamitin domin tabbatarwa, inda ’yan majalisa suka amince ba tare da wata adawa ba kafin su amince da tura sojojin ta hanyar kada kuri’ar murya karo na biyu.

A jawabin sa, Akpabio ya yabawa Shugaba Tinubu bisa ɗaukar matakan da suka tabbatar da zaman lafiya a yankin da kuma bin ka’idojin kundin tsarin mulki ta hanyar neman amincewar majalisa, ko da bayan tura sojojin cikin gaggawa.

“Wannan mataki ne da ya zama dole. Shugaban Ƙasa ya yi aiki ne domin kare tsaron ƙasa da kuma kare dimokuraɗiyya a yammacin Afirka. Barazana ga kasa ɗaya barazana ce ga kowa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa za a isar da kudurin majalisar ga Shugaban Ƙasa nan take.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji
  • Majalisar Dattawa Ta Bawa Tunubu Damar Kai Sojoji Zuwa Kasar Benin
  • DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso