Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa
Published: 16th, April 2025 GMT
Gwamnatin Amurka ta amince da shirin mikawa HKI dubban boma-bomai saboda kashe falasdinawa a Gaza.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, sojojin HKI suna jiran isowar boma-bomai daga kasar Amurka don fara wani aikin soje na musamman a Gaza. Saboda kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.
Wata majiyar HKI, yahudawa ta fadawa kamfanin dillancin labaran ‘Ynetnews’ kan cewa sojojin sama na HKI su na dakon isowar boma-bomai har 3000 daga kasar Amurka a cikin yan makonni masu zuwa.
Labarin ya kara da cewa rundunar ta na son ta gudanar da ayyukan soje mai fadin gaske a kan Falasdinwa wanda ya zai kawo karshen Hamas ya kuma kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.
Labarin ya kara da cewa gwamnatin kasar Amurka ta na shirin aiko da wani karin boma –bomai har 10,000 nan gaba. Yahuda zasu yi amfani da wadannan boma-boman don fadada ayyukansu a yankin, wadanda suka hada da Siriya da Lebanon da kuma ita Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
Kungiyar Falasdinawa ta Jihadul Islami a Gaza, ta bada sanarwan halaka ko jikatar sojojin yahudawan Sahyoniyya 40 a gaza a wani tarko mai sarkakiyan da suka dana masu.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar Saraya Qudus” reshen soje na kungiyar Jihadul Islamim yana fadar haka a jiya Jumma’a.
Daya daga cikin kwamnadojin dakarun ya bayyana cewa da farko halakar yahudawan ta faru ne a garin Gaza a kuma unguwar shuja’iyya. Inda da farko suka halaka sojojin yahudawa kimani 10 a cikin wani ginin da suka shiga cikinsa tare da amfani da makamai mai linzami, sannan a wani gidan
Sannan waso sojojin kimani 20 sun halaka ko sun ji rauni a lokacin dakarun suka yi am,fani da makamin TBG wanda yake watsa isakar gas da ruwa da kuma gari a inda ya fashe don kona jikin wadanda ya fashe a cikinsu.
Na uku kuma sun tana nakiyoyi masu karfi kan tankar yaki dauke da akalla sojojin yahudawa 6 suka kone .
Labarin ya kara da cewa sojojin makiya a irin wannan halin sun kasa daukar wani mataki in banda gudu daga wurin. Daga karshe ba abinda zaka gani sai gawakin sojoji a waste a yankin.