Reshen soja na kungiyar Hamas wato rundunar Izzuddin Qassam, ya gargadi iyalan fursinonin yahudawan Sahyoniyya wadanda take tsare da su a Gaza kan cewa yayansu zasu koma hannunsu gawaki, saboda irin yadda HKI take kara yawaita Jefa boma-boman a kan Falasdinawa a Gaza.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto  wani mai magana da yawan dakarun yana fadar haka a wani fai-fai bidiyo da rundunar ta watsa a yanar gizo a jiya talata.

Dakarun suna kira ga iyalan yahudawan da su yi shirin karban gawakin yayansu a cikin akwatunan gawaki, wannan kuma saboda yadda jiragen yakin HKI suke kai hare-hare babu kakkautawa kan gaza ba tare da bambanta tsakanin  yara da mata da sauransu ba.

Sakon Bidiyon yana cewa (Ya ku iyalan fursinonin ku yi shirin karban gawakin yan uwanku cikin akwatunan gawaki, tare da ganin yadda naman jikinsu a tarwatse, saboda gwamnatinku ta yanke shawarar kashe su a Gaza, don haka ku jira ku gani’.

Wannan sanarwan tana zuwa ne bayan da kungiyar ta bada sanarwan cewa ta kasa samun labarin bangaren dakarun kungiyar wadanda suke kula fursinoni don sanin halin da suke ciki, don mai yuwa an halaksu.

Daga cikin fursinonin da dakarun suka rasa inda yake dai, shi ne Edan Alexander bayahude kuma ba’amerike.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya

Rundunar Sojin Saman Najeriya (NAF), ta ce ta taka muhimmiyar rawa wajen daƙile yunƙurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin, bayan wasu sojoji sun bayyana hamɓarar da Gwamnatin Shugaba Patrice Talon.

Gungun sojojin, sun bayyana cewa ta rushe gwamnati tare da dakatar da kundin tsarin mulki, da rufe iyakokin ƙasar.

An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano

Sun kuma ayyana Laftanar Kanar Tigri Pascal a matsayin Shugaban gwamnatin soja.

Daga baya gwamnatin Benin ta sanar da cewa sojojin ba su yi nasarar yin juyin mulkin ba.

Rahotanni sun nuna cewa jiragen yaƙin Najeriya sun shiga ƙasar domin kare dimokuraɗiyya, duk da cewa babu cikakkun bayanai ba.

NAF, ta tabbatar da cewa ta yi aiki a Benin bisa yarjejeniyar tsaro ta ECOWAS.

“Sojojin Saman Najeriya sun yi aiki a Jamhuriyar Benin bisa ƙa’idojin ECOWAS da umarnin Rundunar Tsaro ta Yanki,” in ji Air Commodore Ehimen Ejodame.

ECOWAS, ta yi Allah-wadai da yunƙurin juyin mulkin, tare da cewa za ta kare dimokuraɗiyyar ƙasar idan buƙatar hakan ta taso.

“ECOWAS za ta tallafa wa gwamnati da al’ummar Benin, har da tura rundunar tsaro ta yankin, domin kare kundin tsarin mulki da ikon ƙasar,” in ji sanarwar ECOWAS.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Yadda Abincin Da Mutane Ke Ci Ke Zamewa Guba
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin
  • Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya
  • An gano gawar malamin Islamiyya da ya ɓace a Neja
  • Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi)
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167
  •  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda