Hamas Ta Fadawa Iyalan Yahudawan Da Take Tsare Dasu A Gaza Kan Cewa ‘Ya’yansu Zasu Koma A Cikin Akwatunan Gawaki
Published: 16th, April 2025 GMT
Reshen soja na kungiyar Hamas wato rundunar Izzuddin Qassam, ya gargadi iyalan fursinonin yahudawan Sahyoniyya wadanda take tsare da su a Gaza kan cewa yayansu zasu koma hannunsu gawaki, saboda irin yadda HKI take kara yawaita Jefa boma-boman a kan Falasdinawa a Gaza.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wani mai magana da yawan dakarun yana fadar haka a wani fai-fai bidiyo da rundunar ta watsa a yanar gizo a jiya talata.
Dakarun suna kira ga iyalan yahudawan da su yi shirin karban gawakin yayansu a cikin akwatunan gawaki, wannan kuma saboda yadda jiragen yakin HKI suke kai hare-hare babu kakkautawa kan gaza ba tare da bambanta tsakanin yara da mata da sauransu ba.
Sakon Bidiyon yana cewa (Ya ku iyalan fursinonin ku yi shirin karban gawakin yan uwanku cikin akwatunan gawaki, tare da ganin yadda naman jikinsu a tarwatse, saboda gwamnatinku ta yanke shawarar kashe su a Gaza, don haka ku jira ku gani’.
Wannan sanarwan tana zuwa ne bayan da kungiyar ta bada sanarwan cewa ta kasa samun labarin bangaren dakarun kungiyar wadanda suke kula fursinoni don sanin halin da suke ciki, don mai yuwa an halaksu.
Daga cikin fursinonin da dakarun suka rasa inda yake dai, shi ne Edan Alexander bayahude kuma ba’amerike.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rizai: Mun Harbo Jirage Kanana Da Manya 80 Na ‘Yan Sahayoniya
Tsohon kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Birgediya Muhsin Rizai, ya sanar da cewa; Dakarun IRGC sun yi nasarar harbo jirage manya da marasa matuki na HKI har guda 80, kuma da akwai baraguzai 32 daga cikinsu da ake rike da su.
Birgediya Rizai ya kuma kara da cewa; Daga cikin wadanda aka harbo din da akwai samfurin “Hermes” da “Hermon” da sune kira ta karshe da ‘yan sahayoniya suke takama da su.
Birgediya Muhsin Rizai wanda memba ne a majalisar fayyace maslahar tsarin musulinci ta Iran, wanda tashar talbijin ta yi hira da shi da marecen jiya Talata, ya yi Magana akan bangarori da dama na kallafaffen yakin kwanaki 12 inda ya ce:” Gabanin mu yi bitar yadda yakin ya kasance, ya zama wajibi mu yi Magana akan cewa, farfagandar da su ka yi, saboda matsin lambar da su ka rika fuskanta ne a cikin gida da kuma a Amurka sannan kuma a fagen duniya. Hakika ita ce Isra’ila ta ci kiasa a yakin. Matsin lambar ya kai ga cewa, Trump ya mayarwa da tashar talabijin irin CNN martani da cewa: Karya kuke yi, mun yi nasara.”
Musin Rizai ya kuma ce; Idan mu ka duba akan ko sun yi nasara, ko a’a, za mu yi nazari akan asarar kudade bisa abinda ma’aikatar kudi ta HKI ta fitar. Sun bayyana cewa, sun yi asarar kudaden da sun kai dalar Amurka biliyan 20 a cikin kwanaki 12 kadai. Kuma Na’urorin kakkabo makamai masu linzami samfurin Thaad da aka kera a cikin shekaru biyu,sun kare. A cikin kwanaki 12, sun karar da na’urorin da su ka dauki shekaru biyu suna kerawa.”
Birgediya Rizai ya kuma bayyana yadda na’urorin Rada na Iran su ka dauko hotunan jikkata da kakkabo jiragen abokan gaba 80 daga cikinsu da akwai baraguzai 32 da ake rike da su.”