Xi Ya Isa Kuala Lumpur Domin Ziyarar Aiki A Malaysia
Published: 15th, April 2025 GMT
A yammacin yau ranar 15 ga watan Afrilu ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa birnin Kuala Lumpur ta jirgin sama na musamman, domin gudanar da ziyarar aiki a kasar Malaysia.
Xi Jinping ya gabatar da rubutacciyar jawabi a filin tashi da saukar jiragen sama, inda ya ce, yana fatan daukar wannan ziyara a matsayin wata dama ta kara zurfafa dadadden zumuncin dake tsakanin kasashen biyu, da kara amincewa da juna a fannin siyasa a tsakanin bangarorin biyu, da sa kaimi ga yin hadin gwiwa a fannin ayyukan zamanantarwa, da sa kaimi ga yin mu’amala da fahimtar juna a tsakanin al’ummomi, da inganta gina al’umma mai kyakkaywar makomar bai daya tsakanin Sin da Malaysia zuwa wani sabon mataki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An Bayyana Filin Jirgin Sama Minna a Matsayin Mafita Ga Jiragen da ke sauka Abuja
A hukumance gwamnatin tarayya ta ayyana filin jirgin saman Bola Ahmed Tinubu dake Minna a matsayin mafita ga jiragen dake sauka Abuja.
Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo ne ya bayyana hakan a yayin bikin kaddamar da jirgin saman na Overland Airways a filin jirgin sama na BAT dake Minna.
Festus Keyamo ya ce ana shirin daukar matakan da suka wajaba kamar su kwastam, shige da fice, ‘yan sanda, NDLEA da sauran su don sarrafa fasinjoji idan filin jirgin Abuja ya samu matsala.
Gwamnan jihar Neja Mohammed Umar Bago wanda ya yabawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu bisa ci gaba da goyon bayan da yake baiwa jihar, ya bayyana cewa wannan nasara wani kokari ne na hadin kai na ganin an farfado da burin jihar a karkashin sabon tsarin mulkin gwamnatin sa.
A nasa bangaren, Wanda ya kafa kuma Manajan Darakta na Kamfanin Jiragen Sama na Overland, Kyaftin Edward Boyo ya bayyana cewa jirgin wani sabon salo ne da aka saya a matsayin sabon tsarin ci gaba tare da sabbin kayan fasahar zamani a bangaren zirga-zirgar jiragen sama yayin da ya ba da tabbacin samar da ayyuka masu inganci.
A nasa jawabin ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris Malagi wanda ya yaba da ci gaban da gwamnan jihar Neja ya samu na tabbatar da manyan mafarkai ya kara yabawa ministan sufurin jiragen sama kan gagarumin ci gaba da aka samu a fannin.
Mohammed Idris ya jaddada cewa farashin kayan masarufi na raguwa sannu a hankali a kasar nan, biyo bayan dabarun da gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dauka na tabbatar da samar da abinci a Najeriya, tare da ba da tabbacin samun kyakkyawar makoma ga ‘yan kasar.
ALIYU LAWAL.