Leadership News Hausa:
2025-10-16@16:45:16 GMT

Xi Ya Isa Kuala Lumpur Domin Ziyarar Aiki A Malaysia

Published: 15th, April 2025 GMT

Xi Ya Isa Kuala Lumpur Domin Ziyarar Aiki A Malaysia

A yammacin yau ranar 15 ga watan Afrilu ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa birnin Kuala Lumpur ta jirgin sama na musamman, domin gudanar da ziyarar aiki a kasar Malaysia.

 

Xi Jinping ya gabatar da rubutacciyar jawabi a filin tashi da saukar jiragen sama, inda ya ce, yana fatan daukar wannan ziyara a matsayin wata dama ta kara zurfafa dadadden zumuncin dake tsakanin kasashen biyu, da kara amincewa da juna a fannin siyasa a tsakanin bangarorin biyu, da sa kaimi ga yin hadin gwiwa a fannin ayyukan zamanantarwa, da sa kaimi ga yin mu’amala da fahimtar juna a tsakanin al’ummomi, da inganta gina al’umma mai kyakkaywar makomar bai daya tsakanin Sin da Malaysia zuwa wani sabon mataki.

(Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila

Rahotanni sun bayyana cewa wani ƙazamin faɗa ya barke tsakanin wata ƙabilar Palasɗinawa masu ɗauke da makamai da ƙungiyar Hamas a yankin zirin Gaza bayan an kulla yarjejeniyar zaman lafiya da Isra’ila.

A ranar Litinin da aka fara musayar fursunoni tsakanin Hamas da Isra’ila ne rahotanni suka ɓulla game da faɗan da ya ɓarke tsakanin mayaƙan Hamas da ƙabilar Doghmush a ranar Lahadi.

Wani jami’in Hamas ya bayyana cewa an samu asarar rayuka daga kowane ɓangare a yayin musayar wutan daga misalin ƙarfe 9.30 na dare ranar Lahadi.

Wani mazaunin yankin Sebra da ke Birnin Gaza, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP cewa “Mayaƙan Hamas kimanin 200 ne suka zo aka fafata da su, har sai da suka murƙushe ’yan ƙabilar Doghmush.

Issa Bakary Tchiroma ne ya lashe zaɓen Kamaru —’Yan adawa NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?

“Wasu ’yan ƙabilar da mayaƙan Hamas sun rasu a yayin artabun,” in ji shi yana mai neman a dakata sunansa saboda dalilan tsaro.

Wata majiya daga ma’aikatar harkokin cikin gida ta Hamas ta zargi ’yan ƙabilar da yi wa sojojin Isra’ila aiki kuma sun kashe mutane da dama, ta ƙara da cewa an tsare mutum shiga daga danginsu.

Iyalan sun musanta zargin da ake musu na yi wa Isra’ila aiki, amma sun amsa cewa sun kai wasu farmaki ba tare da yin ƙarin haske ba.

Sun kuma zargi Hamas da kai musu hari barkatai, kamar yadda AFP ya ruwaito.

Shugaban kabilar, Abu al-Hassan Doghmush, ya wallafa a Facebook cewa abin “ya kai matakin da in dai kai dan ƙabilarmu ce to a iya harbin ka a ƙafa koma kone maka gida.”

Tun da Hamas ta kwace iko a yankin Gaza a 2007 ta sha fama da kabilu da ƙungiyoyi masu ɗaukar makamai.

A ranar Lahadi ne kungiyar ta sanar da afuwa ga duk kungiyoyin masu laifi, waɗanda ba su aikata kisa a lokacin yaƙin ƙasar da Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana Aikin Tsaftace Unguwar Kwankwasiyya Mataki Na biyu
  • Ana Ta Allah Waddai Da Harin Da Aka Kaiwa Al’umma A Jihar Nasarawa
  • Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 
  • Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia
  • Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles
  • Yansandan Italiya Sun Kara Da Masu Goyon Bayan Falasdinawa A Garin Udine
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa
  • An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 
  • Faɗa ya ɓarke tsakanin Palasɗinawa da Hamas bayan sulhu da Isra’ila
  • NAJERIYA A YAU: Shin Babu Wata Hanyar Magance Matsalolin ASUU Ne Sai Ta Yajin Aiki?