Ya ce sama da mutane 150 ne aka kama da laifin faɗan ɗaba da tashin hankali, tare da ƙwato makamai, miyagun ƙwayoyi da kayan sata.

Ya ƙara da cewa matsalolin faɗan ɗaba da shaye-shaye barazana ce ga zaman lafiyar jama’a da makomar matasa.

Duk da yake kame na da muhimmanci, Bakori ya ce dole ne a bai wa matasa damar samun ilimi, koyon sana’o’i da kuma wasu ayyuka da za su riƙa shagaltar da su zuwa hanya mafi dacewa.

Ya kuma shawarci shugabannin ‘yansanda na ƙananan hukumomi da su riƙa haɗa kai da sarakunan gargajiya da al’ummar yankinsu wajen gano matsalolin tsaro a yankunansu.

“Idan muka haɗa kai da goyon bayan jama’a, babu yadda ‘yan daba za su ci gaba da addabar Kano,” in ji CP Bakori.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda Faɗan Daba Kwamishina

এছাড়াও পড়ুন:

Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano

Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya naɗa babban ɗan uwansa, Alhaji Sanusi Ado Bayero, a matsayin Galadiman Kano, bayan rasuwar Abbas Sanusi.

A gefe guda kuma, Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, wanda ke ta ƙaddamar kan sarautar Kano da Aminu Ado Bayero a gaba kotu, ya naɗa Mannir Sanusi a matsayin Galadiman Kano.

Wannan lamari na nuni da cewa rikicin Sarautar Kano ya ɗauki sabon salo, inda kowanne daga cikin ɓangarori biyun ya naɗa nasa Galadiman Kano, inda masu riƙe da sarautun biyu za su gudanar da ayyukansu daban-daban.

A cikin wasiƙar da ke ɗauke da wannan sanarwar, wadda Alhaji Awaisu Abbas Sanusi, babban jami’in gudanarwa na Majalisar Masarautar Kano ya sanya hannu, naɗin Sanusi Ado Bayero ya biyo bayan taron majalisar da Sarki Aminu ya jagoranta a ranar Laraba, 16 ga Afrilu, 2025.

Yadda matsalar ƙwacen waya da faɗan daba ke addabar Kano Dalilin faɗuwar farashin kayan abinci a kasuwannin Arewa NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”

A baya an naɗa Sanusi a matsayin Chiroman Kano, dan Majalisar Masarautar Kano, kuma Hakimin Gwale a zamanin mahaifinsa Sarki Ado Bayero.

Bayan rasuwar mahaifin nasa a shekarar 2014, a matsayinsa na babban ɗa kuma magaji, an ɗauka cewa Sanusi Ado ne  wanda ya cancanci ya gaje shi, War wasu rahotanni na farko sun sanar da shi a matsayin Sarki.

Sai dai, a ranar 8 ga Yuni, 2014, aka naɗa ɗan ɗan uwansa, Sanusi Lamido Sanusi, a matsayin Sarkin Kano. A sakamakon haka, Sanusi Ado ya ƙi yin mubaya’a a gare shi kuma, don nuna rashin amincewa, kuma ya yanke shawarar barin Kano.

Bayan raba Masarautar Kano, da cire Sarki Sanusi II, da kuma naɗin ƙanensa, Aminu Ado Bayero, a matsayin Sarki na 15 a watan Yulin 2020, an mayar da Sanusi Ado Bayero kan matsyinsa a Majalisar Masarautar Kano kuma aka ba shi sarautar Wamban Kano.

Tarihin Sanusi Ado Bayero

Sanusi kammala digirinsana farko a fannin shari’a a shekarar 1983 kuma an rantsar da shi a matsayin lafiya a shekarar 1984.

Tsohon ma’aikacin Gwamnatin Jihar Kano ne inda ya yi aiki daga 1985 zuwa 2015, har ya kai matsayi mafi girma na Babban Sakataren.

Daga baya aka naɗa shi a matsayin Manajan Daraktan Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Najeriya, muƙamin da ya riƙe har zuwa lokacin da aka cire shi a watan Agustan 2015.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano
  • Aminu Bayero ya naɗa Sanusi a matsayin Galadiman Kano
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
  • Yadda matsalar ƙwacen waya da faɗan daba ke addabar Kano