Kwamishinan ‘Yansandan Kano Ya Nemi Taimakon Sarakunan Gargajiya Wajen Kawo Ƙarshen Faɗan Daba
Published: 15th, April 2025 GMT
Ya ce sama da mutane 150 ne aka kama da laifin faɗan ɗaba da tashin hankali, tare da ƙwato makamai, miyagun ƙwayoyi da kayan sata.
Ya ƙara da cewa matsalolin faɗan ɗaba da shaye-shaye barazana ce ga zaman lafiyar jama’a da makomar matasa.
Duk da yake kame na da muhimmanci, Bakori ya ce dole ne a bai wa matasa damar samun ilimi, koyon sana’o’i da kuma wasu ayyuka da za su riƙa shagaltar da su zuwa hanya mafi dacewa.
Ya kuma shawarci shugabannin ‘yansanda na ƙananan hukumomi da su riƙa haɗa kai da sarakunan gargajiya da al’ummar yankinsu wajen gano matsalolin tsaro a yankunansu.
“Idan muka haɗa kai da goyon bayan jama’a, babu yadda ‘yan daba za su ci gaba da addabar Kano,” in ji CP Bakori.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yansanda Faɗan Daba Kwamishina
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfado Da Filin Jirgin Sama Na Kano
Shugaban Hukumar Gudanarwa Filayen Jiragen Sama ta Kasa (FAAN), Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya sake tabbatar da kudirin Gwamnatin Tarayya na dawo da tsohon martabar Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano.
Dakta Ganduje ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar duba aiki da ya kai filin jirgin a Kano.
Ya jagoranci wata tawaga mai ƙarfi ta jami’an FAAN domin tantance halin da filin jirgin yake ciki yanzu, ciki har da ayyukan da ake gudanarwa da kuma waɗanda aka bari da nufin samar da cikakken tsari na zamani da dorewar ci gaba.
Ya bayyana a matsayin ɗaya daga cikin tsofaffin filayen jiragen sama masu tarihi a Najeriya da yankin Yammacin Afirka, wanda a da yake ɗaya daga cikin manyan cibiyoyin tashi da saukar jirage da ke haɗa Najeriya da sauran sassan duniya.
“Mun zo ne mu gani da idonmu, tsoffin ayyuka da sababbi, domin mu tsara sabuwar hanya ta farfado da wannan fili tare da dawo da matsayinsa cikin fitattun filayen jiragen sama na yankin,” in ji Ganduje.
Ya jaddada cewa hukumar FAAN za ta tabbatar da inganta jin daɗin fasinjoji, kiyaye ƙa’idodin tsaro, da kuma haɓaka ingancin aiki bisa ka’idodin ƙasa da ƙasa.
Dakta Ganduje ya tabbatar da cewa abubuwan da tawagar ta gano a yayin ziyarar za su zama ginshiƙi wajen tsara sabuwar manuniya ta dabarun sake farfado da filin domin ya zama abin koyi a harkar gudanar da filayen jiragen sama da kuma abin ƙarfafa tattalin arzikin Arewa.
Tawagar ta ziyarci sassa daban-daban na filin jirgin, ciki har da zauren sauka da tashin fasinjoji, hanyar tashi da saukar jirage, da kuma rukunin jigilar kaya, domin gano wuraren da ake bukatar gaggawar gyara.
ABDULLAHI JALALUDDEEN, Kano.