Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Yi Watsi Da Matsawa Sauran Kasashe Lamba
Published: 14th, April 2025 GMT
Game da batun cewa ministan tsaron Amurka da sauran manyan jami’ai sun wallafa maganganun dake yada ra’ayin wai “Sin ta kawo barazana”, Lin Jian ya ce, wasu maganganun jami’an bangaren Amurka suna cike da bambancin akida da tunanin yakin cacar baka, gaba daya karya ce.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare.
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
Wani abun lura ma a nan shi ne yadda a matsayinta na kasa mai tasowa ta farko a tarihin duniya da ta cimma nasarar samun wadata cikin lumana, Sin ta samar da wata taswira mai inganci, wadda sauran kasashe masu tasowa za su iya bi domin raya kansu cikin lumana, kuma karkashin hakan ne take ta fitar da shawarwari na ingiza ci gaban duniya bi da bi, irinsu shawarar raya jagorancin duniya da kasar ta gabatar a baya bayan nan. Shawarar da masharhanta da yawa ke ganin na da ma’anar gaske, wajen ingiza adalci, da daidaito a tsarin cudanyar mabanbantan sassan duniya.
A gani na tun da har kasar Sin ta kai ga gina tsari mai gamsarwa na raya kai bisa salon musamman mafi dacewa da yanayinta, wanda kuma yake ta kara samun karbuwa tsakanin kasashen duniya, a halin yanzu, kasar na kan wani matsayi na rarraba kwarewarta tare da sauran abokan tafiya, musamman kasashe masu tasowa. Wanda hakan kyakkyawan misali ne da dukkanin wata kasa a duniyan nan za ta iya lura da shi, yayin da take kokarin bunkasa kanta gwargwadon yanayin da take ciki.
Tabbas, ci gaban kasar Sin mai ban mamaki ya nunawa duniya cewa, kowace kasa na iya samun ci gaba ba tare da murdiya, muzgunawa wasu sassa, ko nuna karfin iko na siyasa ko tattalin arziki ba, maimakon hakan kasar Sin ta nunawa duniya cewa abu ne mai yiwuwa, a samu ci gaba bisa hadin gwiwar cimma moriya tare, ta yadda za a gudu tare a kuma tsira tare.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA